• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Dalilin Da Zai Sanya Wasu Mambobin PDP Ficewa A Jam’iyyar A Bauchi

by Khalid Idris Doya, Sulaiman and CGTN Hausa
5 months ago
in Labarai
0
PDP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PDP da ke mulki a Jihar Bauchi ta tabbatar da cewa bisa kyawawan ayyuka da gwamnatin jihar ke shimfidawa wanda al’ummar jihar suka gamsu da su tare kuma kyakkyawar hadin kai da ke tsakanin mambobin jam’iyyar a jihar, babu wani dalilin da zai sanya wasu su ma ji sha’awar ficewa daga jam’iyyar.

 

Jam’iyyar ta tabbatar da cewa kan mambobinta da shugabanninta a hade suke wanda hakan ne zai tabbatar da irin nasarar da jam’iyyar za ta samu a zaben 2027 da ke tafe.

  • Bayan Fara Binciken $2.96bn, An Samu N80bn A Asusun Tsohon Daraktan Kamfanin NNPCL
  • Dakataccen Gwamnan Ribas Ya Dawo Daga Hutun Makonni Biyu A Kasar Waje

Sakataren watsa labarai na jam’iyyar a matakin Jihar Bauchi, Dakta Dayyabu Chiroma ya shaida wa LEADERSHIP a hirarsa da wakilinmu cewa jam’iyyar za ta samu gagarumin nasara a dukkanin kujeru a jihar sakamakon hadin kai da ayyukan da suke gudanarwa.

 

Labarai Masu Nasaba

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

“Ka san idan za ka yi la’akari da sauran jihohin da suke barin jam’iyyarsu su shiga wata jam’iyya ni a tunanina tsoro ne karawa da babban jam’iyyar adawar da ke jihar ba, yanzu misali a Jihar Delta shi gwamnan jihar ya san daker ya ci zabe a 2023 sannan kuma yana da yakinin idan bai fita daga PDP ya shiga APC ba ba zai iya samun nasara a 2027 ba; to mu in ka yi la’akari da hakan a jam’iyyar mu ta PDP a Jihar Bauchi tun da ake mulki sau daya APC ta samu galba a 2015 sakamakon maja wanda ya ci ko’ina. “Duk gwamnonin PDP da aka yi a Jihar Bauchi ba wanda bai kafa tarihin yin kyawawan ayyuka ba. Idan za ka kwatanta mulkin Ahmad Muazu da Dakta Malam Isa Yuguda ba za ka taba kwatantawa da abun da shi M.A Abubakar ya yi ba, kowa ya sani mulkin APC wanda M.A Abubakar ya yi ba a taba mummunar mulki irinta ba.

 

“Balle kuma yanzu da gwamna Bala Muhammad Abdulkadir ke gudanar da kyawawan ayyuka da kawo ci gaba da kyautata wa jama’a da inganta fannoni daban-daban wanda al’ummar jihar gaba daya sun yi gamsu da kokarinsa ba wani dalilin da wani zai ji sha’awar ficewa daga jam’iyyar.”

 

Ya nuna cewa duk da matsalolin da jam’iyyun siyasa ke fuskanta a Nijeriya bai takaita ga PDP zalla ba, amma ba su ji dadin yadda wasu fitattun mutane ke ficewa daga jam’iyyar ba ciki har da gwamnan jihar Delta, da tsohon gwamnan da ‘yan majalisu tarayya da na jihohi, da shugabannin kananan hukumomi a ce sun bar jam’iyyar PDP ba karamin rashi ba ne.

 

Sai dai ya tabbatar da cewa wannan matakin ba zai shafi nasarar da jam’iyyar ta saba samu a jihar Delta ba, ya tabbatar da cewa PDP ce za ta yi nasara a Delta a zaben 2027 da ke tafe.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin: Adadin Tafiye-tafiye Yayin Ranakun Hutun Murnar Ranar ‘Yan Kwadago Ta Duniya Ya Kafa Tarihi 

Next Post

Amurka Ba Za Ta Cimma Nasara Ta Hanyar Yakin Cinikayya Ba

Related

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

2 hours ago
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
Labarai

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

2 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

4 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

5 hours ago
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
Labarai

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

6 hours ago
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

8 hours ago
Next Post
Amurka Ba Za Ta Cimma Nasara Ta Hanyar Yakin Cinikayya Ba

Amurka Ba Za Ta Cimma Nasara Ta Hanyar Yakin Cinikayya Ba

LABARAI MASU NASABA

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.