• English
  • Business News
Tuesday, June 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Babu Gaskiya A Takardar Da Ke Alaƙanta Gwamnatin Zamfara Da ’Yan Bindiga”

by Musa Muhammad
9 months ago
in Labarai
0
“Babu Gaskiya A Takardar Da Ke Alaƙanta Gwamnatin Zamfara Da ’Yan Bindiga”
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata tarkardar ƙage, wacce aka ce ta fito ne daga gidan gwamnatin jihar Zamfara da ke Gusau, mai ɗauke da sa hannun Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Abubakar Nakwada, ta yi iƙirarin cewa Gwamna Dauda Lawal ya bayar da umurnin a saki Naira Biliyan 1,378,000,000 ga wasu manyan shugabannin ’yan bindiga.

Haka zalika, takardar ta yi zargin cewa kafafen yaɗa labarai irin su Sahara Reporters, Jackson Ude, da sauran su sun amfana da waɗannan kuɗaɗe.

  • Sojoji Sun Sheƙe Ƴan Ta’adda Masu  Yawa A Kaduna Da Zamfara
  • Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Tallafawa Majinyata 1000 Da Abinci Da Kuɗi

To amma yana da muhimmanci a fahimci cewa, dukkan waɗanda aka yi wa ƙazafi a cikin wannan takardar sharri, su ne waɗanda suka ɗauki labaran fallasa alaƙanta Bello Turji da Alhaji Bello Mattawalle, Ministan Tsaro, da badaƙalar Alhaji Bashir Hadejia da aka kama da laifin ɗaukar nauyin ta’addanci da safarar makamai da zinare da dai sauransu.

Wannan ne ta sa Sakataren gwamnatin Jihar Zamfara, Alhaji Abubakar Nakwada, yayin da yake mayar da martani kan wannan takarda, ya ce “Wannan takarda mara tushe ta alaƙanta gwamnatin Zamfara da kiran zaman lafiya da Bello Turji, wanda ya kasance sanannen shugaban ’yan bindiga ne ya yi.

Gwamnatin Gwamna Dauda Lawal ta yi kakkausar suka, inda ta musanta yin sulhu da ‘yan ta’adda, kuma ta jaddada cewa takardar, wani yunƙuri ne da aka ƙirƙira da gangan da nufin gurgunta ƙoƙarin da gwamnatin jihar ke yi na samar da tsaro.

Labarai Masu Nasaba

Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

Don haka a fahimci wannan labarin da cewa ƘARYA ce, kuma yaudara ce.

Ita ma jam’iyyar AAC ta Omoyele Sowore, wanda kuma shi ne mawallafin jaridar Sahararepoters, wacce kuma tana cikin waɗanda aka ce sun amfana da waɗannan kuɗaɗe, ta fito fili ta yi tofin Allah-tsine da ganin wannan takarda, wacce ta ce ƙarya ce tsagwaronta.

Ɗan takarar Shugaban ƙasa na Jam’iyyar ta AAC, wanda ya ke kuma shi ne shugabanta, Omoyele Sowore ya ce, “Ya wajaba a gare mu mu nusar da jama’a irin sabon salon farfagandar da Bola Tinubu ya fito da ita na zubar da mutuncin mani da mutunci, ni da SaharaReporters.

“Wata takardar cikin gida, wacce aka alaƙanta da Sakataren gwamnatin jihar Zamfara, tana nan tana yawo a tsakanin jama’a, aka ce wai an ware wasu maƙudan kuɗaɗe don a raba wa ‘yan ta’adda da wasu kafafen watsa labarai.

Sowore ya ce, wannan ƙarya ce, bai san da wani abu mai kama da haka ba.

Shi ma, ɗaya daga cikin waɗanda aka ambaci sunayen su a waccan ƙagaggar takarda, Jacson Ude, a shafin sa na tweeter (X), ya yi watsi da wannan batu, inda ya ɗora laifin kan tsohon Kwamishinan yaɗa labarai na gwamnatin Bello Matawalle.

Jackson Ude ya yi zargin cewa Tsohon Kwamishinan yaɗa labaran, ya kasance ya ɓoye kansa a wani wuri, inda ba abin da ya ke yi sai ƙage-ƙagen ƙarairayi kan duk waɗanda suka ya ƙi gwammatin Matawalle.

Don haka ya ce, wannan takarda sam ba ta da tushe balle makama, ƙarya ce tsagwaronta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BanditsTerroristZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

CIFIT: Dandalin Samun Wadata Ta Bai Daya

Next Post

Kungiyar Miyatti Allah Ta Haramta Kiwon Dare A Jihar Kwara

Related

Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet
Manyan Labarai

Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

2 minutes ago
Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba
Labarai

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

1 hour ago
Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa
Manyan Labarai

Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa

2 hours ago
FRSC Ta Fara Binciken Hatsarin Motar Da Ya Yi Ajalin ’Yan Wasan Kano 22
Labarai

FRSC Ta Fara Binciken Hatsarin Motar Da Ya Yi Ajalin ’Yan Wasan Kano 22

3 hours ago
FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista
Manyan Labarai

FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista

4 hours ago
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara
Labarai

Jiragen Yakin NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 20, ‘Yan Banga 2 A Zamfara

13 hours ago
Next Post
Kungiyar Miyatti Allah Ta Haramta Kiwon Dare A Jihar Kwara

Kungiyar Miyatti Allah Ta Haramta Kiwon Dare A Jihar Kwara

LABARAI MASU NASABA

Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

June 3, 2025
Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

June 3, 2025
Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa

Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa

June 3, 2025
FRSC Ta Fara Binciken Hatsarin Motar Da Ya Yi Ajalin ’Yan Wasan Kano 22

FRSC Ta Fara Binciken Hatsarin Motar Da Ya Yi Ajalin ’Yan Wasan Kano 22

June 3, 2025
FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista

FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista

June 3, 2025
Kasar Sin: Amurka Ta Yi Matukar Kawo Cikas Ga Yarjejeniyar Da Aka Cimma A Tattaunawar Geneva

Kasar Sin: Amurka Ta Yi Matukar Kawo Cikas Ga Yarjejeniyar Da Aka Cimma A Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

June 2, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

Jiragen Yakin NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 20, ‘Yan Banga 2 A Zamfara

June 2, 2025
Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

June 2, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.