ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Babu Gaskiya A Takardar Da Ke Alaƙanta Gwamnatin Zamfara Da ’Yan Bindiga”

by Musa Muhammad
2 years ago
Zamfara

Wata tarkardar ƙage, wacce aka ce ta fito ne daga gidan gwamnatin jihar Zamfara da ke Gusau, mai ɗauke da sa hannun Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Abubakar Nakwada, ta yi iƙirarin cewa Gwamna Dauda Lawal ya bayar da umurnin a saki Naira Biliyan 1,378,000,000 ga wasu manyan shugabannin ’yan bindiga.

Haka zalika, takardar ta yi zargin cewa kafafen yaɗa labarai irin su Sahara Reporters, Jackson Ude, da sauran su sun amfana da waɗannan kuɗaɗe.

  • Sojoji Sun Sheƙe Ƴan Ta’adda Masu  Yawa A Kaduna Da Zamfara
  • Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Tallafawa Majinyata 1000 Da Abinci Da Kuɗi

To amma yana da muhimmanci a fahimci cewa, dukkan waɗanda aka yi wa ƙazafi a cikin wannan takardar sharri, su ne waɗanda suka ɗauki labaran fallasa alaƙanta Bello Turji da Alhaji Bello Mattawalle, Ministan Tsaro, da badaƙalar Alhaji Bashir Hadejia da aka kama da laifin ɗaukar nauyin ta’addanci da safarar makamai da zinare da dai sauransu.

ADVERTISEMENT

Wannan ne ta sa Sakataren gwamnatin Jihar Zamfara, Alhaji Abubakar Nakwada, yayin da yake mayar da martani kan wannan takarda, ya ce “Wannan takarda mara tushe ta alaƙanta gwamnatin Zamfara da kiran zaman lafiya da Bello Turji, wanda ya kasance sanannen shugaban ’yan bindiga ne ya yi.

Gwamnatin Gwamna Dauda Lawal ta yi kakkausar suka, inda ta musanta yin sulhu da ‘yan ta’adda, kuma ta jaddada cewa takardar, wani yunƙuri ne da aka ƙirƙira da gangan da nufin gurgunta ƙoƙarin da gwamnatin jihar ke yi na samar da tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Don haka a fahimci wannan labarin da cewa ƘARYA ce, kuma yaudara ce.

Ita ma jam’iyyar AAC ta Omoyele Sowore, wanda kuma shi ne mawallafin jaridar Sahararepoters, wacce kuma tana cikin waɗanda aka ce sun amfana da waɗannan kuɗaɗe, ta fito fili ta yi tofin Allah-tsine da ganin wannan takarda, wacce ta ce ƙarya ce tsagwaronta.

Ɗan takarar Shugaban ƙasa na Jam’iyyar ta AAC, wanda ya ke kuma shi ne shugabanta, Omoyele Sowore ya ce, “Ya wajaba a gare mu mu nusar da jama’a irin sabon salon farfagandar da Bola Tinubu ya fito da ita na zubar da mutuncin mani da mutunci, ni da SaharaReporters.

“Wata takardar cikin gida, wacce aka alaƙanta da Sakataren gwamnatin jihar Zamfara, tana nan tana yawo a tsakanin jama’a, aka ce wai an ware wasu maƙudan kuɗaɗe don a raba wa ‘yan ta’adda da wasu kafafen watsa labarai.

Sowore ya ce, wannan ƙarya ce, bai san da wani abu mai kama da haka ba.

Shi ma, ɗaya daga cikin waɗanda aka ambaci sunayen su a waccan ƙagaggar takarda, Jacson Ude, a shafin sa na tweeter (X), ya yi watsi da wannan batu, inda ya ɗora laifin kan tsohon Kwamishinan yaɗa labarai na gwamnatin Bello Matawalle.

Jackson Ude ya yi zargin cewa Tsohon Kwamishinan yaɗa labaran, ya kasance ya ɓoye kansa a wani wuri, inda ba abin da ya ke yi sai ƙage-ƙagen ƙarairayi kan duk waɗanda suka ya ƙi gwammatin Matawalle.

Don haka ya ce, wannan takarda sam ba ta da tushe balle makama, ƙarya ce tsagwaronta.

Zamfara
Musa Muhammad
+ postsBio
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    Ina Rokon Allah Ya Sa Na Kammala Sana’ar Fim Cikin Mutunci – Jarumi Sadik
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    Atiku Ga ‘Yan Inugu: Za Mu Samar Muku Da Romon Dimokraɗiyya Idan Kuka Zaɓe Mu
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    2023: Atiku Ya Sha Alwashin Ƙara Wa Jihohi Da Ƙananan Hukumomi Ƙarfin Iko
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    Ambaliyar Ruwa: Gwamnati Ta Fara Kai Agajin Tan 12,000 Na Abinci Jigawa Da Anambra

MASU ALAKA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Next Post
Kungiyar Miyatti Allah Ta Haramta Kiwon Dare A Jihar Kwara

Kungiyar Miyatti Allah Ta Haramta Kiwon Dare A Jihar Kwara

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.