• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Sauran Burbushin ‘Yan Ta’addan Lakurawa A Arewa Maso Yamma – Ministan Tsaro

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
5 months ago
in Labarai
0
A Yanzu Nijeriya Na Sayar Da Makamai Ga Kasashen Afrika – Matawalle
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Karamin ministan tsaro, Hon. Bello Mohammed Matawalle, ya shelanta cewa gabaki daya babu sauran burbushin tsagerun Lakurawa a yankin Arewa Maso Yamma a halin yanzu.

Da yake ganawa da manema labarai a Gusau a ranar Lahadi, tsohon gwamnan Jihar Zamfara ya ce, dakarun sojoji sun hallaka gungun ‘yan ta’addan, sannan sun kuma tarwatsa sansanoninsu da kwato bindigogi da alburusai daga hannunsu.

  • Yadda Turmutsutsin Rabon Kayan Abinci Ya Dagula Karsashin Kirsimeti
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama Tare Da Tarwatsa Sansanoninsu A Katsina

Ya kuma ce wadannan ‘yan ta’addan ba ma ‘yan Nijeriya ba ne, sun fito ne kawai daga Burkina Faso da Mali domin su janyo tashin tashina a Nijeriya.

“Mun gama da su a yankin Arewa maso yamma. Duk wanda ke magana kan tsagerun Lakurawa yana yi ne kawai domin ya bata kima da mutuncin gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro,” ministan ya shaida.

Ya ci gaba da cewa, mutane kawai sun dukufa wajen yayada labarai na kanzon kurege domin sanya razana da firgici a zukatan al’umma, sai ya kalubalanci ‘yan jarida musamman ‘yan Soshal Midiya da su daina amincewa da irin wadannan ikirarin ba tare da tantance bayanan ba.

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

“A kullum sojoji na kashe ‘yan fashin daji da ‘yan bindiga dadi. Amma ba za ka ga masu s’ocial media’ na yayata hakan ba.

“Muna sane mazauna kauyuka na bai wa ‘yan jarida bayanai marasa tushe kan ayyukan masu garkuwa da mutane ake a jihar nan domin nuna gazawar gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

“Amma ba za mu mika wuya ga barazanarsu ba. Gwamnatin Tinubu a shirye take ta kawo karshen dukkanin ‘yan fashin daji a Arewa maso yammacin kasar nan a karshen 2025.

“Kare rayuka da dukiyar al’umma shi ne muhimmin abu da gwamnatin tarayya ta sanya a gaba, kuma za mu kara sanya azama kan wannan manufar,” ya shaida.

Ministan ya nemi ‘yan Nijeriya da su yi fatali da labarai karya da makiyan zaman lafiya da ci gaban kasar nan ke yadawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Turmutsutsin Rabon Kayan Abinci Ya Dagula Karsashin Kirsimeti

Next Post

Tsarin Kwalliya Da Adon Manzon Allah (SAW)

Related

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar
Labarai

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

56 minutes ago
Gwamnan kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

3 hours ago
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina
Labarai

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

3 hours ago
An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya
Labarai

An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

4 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

16 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati
Labarai

Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

17 hours ago
Next Post
Manzon Allah

Tsarin Kwalliya Da Adon Manzon Allah (SAW)

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

June 1, 2025
Gwamnan kano

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

June 1, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

June 1, 2025
An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

June 1, 2025
Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

June 1, 2025
Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo

Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo

June 1, 2025
Yadda Za Ki Hada Funkasonki

Yadda Za Ki Hada Funkasonki

June 1, 2025
Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.