ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Sauran Burbushin ‘Yan Ta’addan Lakurawa A Arewa Maso Yamma – Ministan Tsaro

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
11 months ago
Lakurawa

Karamin ministan tsaro, Hon. Bello Mohammed Matawalle, ya shelanta cewa gabaki daya babu sauran burbushin tsagerun Lakurawa a yankin Arewa Maso Yamma a halin yanzu.

Da yake ganawa da manema labarai a Gusau a ranar Lahadi, tsohon gwamnan Jihar Zamfara ya ce, dakarun sojoji sun hallaka gungun ‘yan ta’addan, sannan sun kuma tarwatsa sansanoninsu da kwato bindigogi da alburusai daga hannunsu.

  • Yadda Turmutsutsin Rabon Kayan Abinci Ya Dagula Karsashin Kirsimeti
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama Tare Da Tarwatsa Sansanoninsu A Katsina

Ya kuma ce wadannan ‘yan ta’addan ba ma ‘yan Nijeriya ba ne, sun fito ne kawai daga Burkina Faso da Mali domin su janyo tashin tashina a Nijeriya.

ADVERTISEMENT

“Mun gama da su a yankin Arewa maso yamma. Duk wanda ke magana kan tsagerun Lakurawa yana yi ne kawai domin ya bata kima da mutuncin gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro,” ministan ya shaida.

Ya ci gaba da cewa, mutane kawai sun dukufa wajen yayada labarai na kanzon kurege domin sanya razana da firgici a zukatan al’umma, sai ya kalubalanci ‘yan jarida musamman ‘yan Soshal Midiya da su daina amincewa da irin wadannan ikirarin ba tare da tantance bayanan ba.

LABARAI MASU NASABA

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

“A kullum sojoji na kashe ‘yan fashin daji da ‘yan bindiga dadi. Amma ba za ka ga masu s’ocial media’ na yayata hakan ba.

“Muna sane mazauna kauyuka na bai wa ‘yan jarida bayanai marasa tushe kan ayyukan masu garkuwa da mutane ake a jihar nan domin nuna gazawar gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

“Amma ba za mu mika wuya ga barazanarsu ba. Gwamnatin Tinubu a shirye take ta kawo karshen dukkanin ‘yan fashin daji a Arewa maso yammacin kasar nan a karshen 2025.

“Kare rayuka da dukiyar al’umma shi ne muhimmin abu da gwamnatin tarayya ta sanya a gaba, kuma za mu kara sanya azama kan wannan manufar,” ya shaida.

Ministan ya nemi ‘yan Nijeriya da su yi fatali da labarai karya da makiyan zaman lafiya da ci gaban kasar nan ke yadawa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama
Manyan Labarai

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya
Labarai

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

November 15, 2025
Next Post
Manzon Allah

Tsarin Kwalliya Da Adon Manzon Allah (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025
Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba

Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba

November 15, 2025
Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin

Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
Yadda Ake Miyar Margi (Margi Special)

Yadda Ake Miyar Margi (Margi Special)

November 15, 2025
Yadda Za Ku Gyara Kanku

Yadda Za Ku Gyara Kanku

November 15, 2025
NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.