• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Sauran Burbushin ‘Yan Ta’addan Lakurawa A Arewa Maso Yamma – Ministan Tsaro

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
A Yanzu Nijeriya Na Sayar Da Makamai Ga Kasashen Afrika – Matawalle
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Karamin ministan tsaro, Hon. Bello Mohammed Matawalle, ya shelanta cewa gabaki daya babu sauran burbushin tsagerun Lakurawa a yankin Arewa Maso Yamma a halin yanzu.

Da yake ganawa da manema labarai a Gusau a ranar Lahadi, tsohon gwamnan Jihar Zamfara ya ce, dakarun sojoji sun hallaka gungun ‘yan ta’addan, sannan sun kuma tarwatsa sansanoninsu da kwato bindigogi da alburusai daga hannunsu.

  • Yadda Turmutsutsin Rabon Kayan Abinci Ya Dagula Karsashin Kirsimeti
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama Tare Da Tarwatsa Sansanoninsu A Katsina

Ya kuma ce wadannan ‘yan ta’addan ba ma ‘yan Nijeriya ba ne, sun fito ne kawai daga Burkina Faso da Mali domin su janyo tashin tashina a Nijeriya.

“Mun gama da su a yankin Arewa maso yamma. Duk wanda ke magana kan tsagerun Lakurawa yana yi ne kawai domin ya bata kima da mutuncin gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro,” ministan ya shaida.

Ya ci gaba da cewa, mutane kawai sun dukufa wajen yayada labarai na kanzon kurege domin sanya razana da firgici a zukatan al’umma, sai ya kalubalanci ‘yan jarida musamman ‘yan Soshal Midiya da su daina amincewa da irin wadannan ikirarin ba tare da tantance bayanan ba.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

“A kullum sojoji na kashe ‘yan fashin daji da ‘yan bindiga dadi. Amma ba za ka ga masu s’ocial media’ na yayata hakan ba.

“Muna sane mazauna kauyuka na bai wa ‘yan jarida bayanai marasa tushe kan ayyukan masu garkuwa da mutane ake a jihar nan domin nuna gazawar gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

“Amma ba za mu mika wuya ga barazanarsu ba. Gwamnatin Tinubu a shirye take ta kawo karshen dukkanin ‘yan fashin daji a Arewa maso yammacin kasar nan a karshen 2025.

“Kare rayuka da dukiyar al’umma shi ne muhimmin abu da gwamnatin tarayya ta sanya a gaba, kuma za mu kara sanya azama kan wannan manufar,” ya shaida.

Ministan ya nemi ‘yan Nijeriya da su yi fatali da labarai karya da makiyan zaman lafiya da ci gaban kasar nan ke yadawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Turmutsutsin Rabon Kayan Abinci Ya Dagula Karsashin Kirsimeti

Next Post

Tsarin Kwalliya Da Adon Manzon Allah (SAW)

Related

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

6 minutes ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

3 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

14 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

20 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

21 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

22 hours ago
Next Post
Manzon Allah

Tsarin Kwalliya Da Adon Manzon Allah (SAW)

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.