• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Sauran Burbushin ‘Yan Ta’addan Lakurawa A Arewa Maso Yamma – Ministan Tsaro

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
10 months ago
Lakurawa

Karamin ministan tsaro, Hon. Bello Mohammed Matawalle, ya shelanta cewa gabaki daya babu sauran burbushin tsagerun Lakurawa a yankin Arewa Maso Yamma a halin yanzu.

Da yake ganawa da manema labarai a Gusau a ranar Lahadi, tsohon gwamnan Jihar Zamfara ya ce, dakarun sojoji sun hallaka gungun ‘yan ta’addan, sannan sun kuma tarwatsa sansanoninsu da kwato bindigogi da alburusai daga hannunsu.

  • Yadda Turmutsutsin Rabon Kayan Abinci Ya Dagula Karsashin Kirsimeti
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama Tare Da Tarwatsa Sansanoninsu A Katsina

Ya kuma ce wadannan ‘yan ta’addan ba ma ‘yan Nijeriya ba ne, sun fito ne kawai daga Burkina Faso da Mali domin su janyo tashin tashina a Nijeriya.

“Mun gama da su a yankin Arewa maso yamma. Duk wanda ke magana kan tsagerun Lakurawa yana yi ne kawai domin ya bata kima da mutuncin gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro,” ministan ya shaida.

Ya ci gaba da cewa, mutane kawai sun dukufa wajen yayada labarai na kanzon kurege domin sanya razana da firgici a zukatan al’umma, sai ya kalubalanci ‘yan jarida musamman ‘yan Soshal Midiya da su daina amincewa da irin wadannan ikirarin ba tare da tantance bayanan ba.

LABARAI MASU NASABA

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

“A kullum sojoji na kashe ‘yan fashin daji da ‘yan bindiga dadi. Amma ba za ka ga masu s’ocial media’ na yayata hakan ba.

“Muna sane mazauna kauyuka na bai wa ‘yan jarida bayanai marasa tushe kan ayyukan masu garkuwa da mutane ake a jihar nan domin nuna gazawar gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

“Amma ba za mu mika wuya ga barazanarsu ba. Gwamnatin Tinubu a shirye take ta kawo karshen dukkanin ‘yan fashin daji a Arewa maso yammacin kasar nan a karshen 2025.

“Kare rayuka da dukiyar al’umma shi ne muhimmin abu da gwamnatin tarayya ta sanya a gaba, kuma za mu kara sanya azama kan wannan manufar,” ya shaida.

Ministan ya nemi ‘yan Nijeriya da su yi fatali da labarai karya da makiyan zaman lafiya da ci gaban kasar nan ke yadawa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Labarai

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI
Manyan Labarai

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
Next Post
Manzon Allah

Tsarin Kwalliya Da Adon Manzon Allah (SAW)

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.