• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wanda Zai Iya Rushe Masarautun Kano, Martanin Ganduje Ga Kwankwaso

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Babu Wanda Zai Iya Rushe Masarautun Kano, Martanin Ganduje Ga Kwankwaso
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Ganduje ya sake nanata cewa sabbin masarautu hudu da gwamnatinsa ta kirkiro suna nan daram.

Gwamnan ya bayyana haka ne a ranar Litinin yayin bikin ranar ma’aikata da aka gudanar a filin wasa na Sani Abacha da ke Kano.

  • An Kwaso Daukacin Daliban Nijeriya Da Suka Makale A Khartoum – Kungiyar Dalibai
  • Gwamnatin Edo Za Ta Kashe Naira Biliyan 6 Wajen Gyaran Makarantun Sakandare A Jihar 

Kalaman nasa na zuwa ne kwanaki kadan bayan da jagoran jam’iyyar NNPP na kasa, Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana a wani faifan bidiyo cewa gwamnatin Abba Yusuf mai jiran gado za ta sake duba salon mulkin masarautun Kano.

Sai dai Gwamna Ganduje wanda ya raba masarautun Kano gida biyar sannan ya tsige Sarkin Kano Muhammadu Sunusi na wancan lokacin ya bayyana cewa sabbin masarautun guda hudu alama ce ta hadin kai, ci gaba da jin dadin al’umma.

Ya kara da cewa an kirkiro masarautun ne domin karrama al’ummar yankunan da kuma dawo da martabar masarautun gargajiya.

Labarai Masu Nasaba

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

“Duk wanda ya ziyarci hedikwatar wadannan sabbin masarautun zai yarda cewa mun kawo ci gaba a wadannan wuraren. Mun kirkire su ne domin karrama mutanen wadannan yankuna,” in ji Ganduje.

Ya kuma tabbatar wa da al’ummar Kano cewa masarautu na dindindin ne kuma sun zo su zauna, ya kuma kara da cewa duk wanda ya yi yunkurin rusa su Allah ba zai kawo shi Jihar Kano ba.

“Ko ba ma gwamnati muna addu’a kuma za mu ci gaba da addu’ar Allah ya kare wadannan masarautun daga dukkan sharri. Na gode muku duka,” in ji shi.

Samar da sabbin masarautun dai ya kasance batun cece-kuce a Kano tun daga 2020, inda wasu ke goyon bayan matakin yayin da wasu ke adawa da shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbbaGandujegwamnatikanoKwankwasoMasarautu
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Riƙa Tabbatar Da Hukunci Ga Masu Yaɗa Labarun Ƙanzon Kurege – CI Sunday James

Next Post

Shugaban Syria Ya Jinjinawa Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

Related

Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

11 hours ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

17 hours ago
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja
Manyan Labarai

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

18 hours ago
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa
Manyan Labarai

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

19 hours ago
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa
Manyan Labarai

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

20 hours ago
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

1 day ago
Next Post
Shugaban Syria Ya Jinjinawa Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

Shugaban Syria Ya Jinjinawa Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.