• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wani Abu Da Zai Hana Mika Mulki A Ranar 29 Ga Mayu –Gwamnatin Tarayya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Babu Wani Abu Da Zai Hana Mika Mulki A Ranar 29 Ga Mayu –Gwamnatin Tarayya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta gargadi duk masu shirin kawo tarnaki ga tsarin mika mulki da shugaban kasa mai ci Muhammadu Buhari zai yi ga zababben shugaban kasa, Asiwaju Ahmed Bola Tinubu a ranar 29 ga watan Mayu.

Sakataren gwamnatin tarayya, Mista Boss Mustapha shi ya yi wannan gargadin a ranar Talata a Abuja, yayin da yake bayani kan ayyukan kwamitin mika mulki na shugaban kasa, ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa tsarin mika mulki ya kankama, kuma a ranar 29 ga watan Mayu za a mika mulki ga sabon shugaban kasar cikin lumana.

  • Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu

Ya kuma bayyana cewa bayan ayyana Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a matsayin zababben shugaban kasa, kwamitin mika mulki ta bukace shi da ya zabo wakilansa ga majalisar kamar yadda dokar zartarwa ta tanada.

Don haka, Mustapha ya ce zababben shugaban kasa ya zabi Atiku Bagudu, Gwamnan Jihar Kebbi da kuma Cif Olawale Edun wadanda tun daga lokacin suka shiga aikin gadan-gadan.

Ya kuma bayyana cewa a yanzu haka zababben shugaban kasa ya tare a gidan tsaro, sannan kuma an tura jami’an tsaro na ma’aikatar harkokin wajen kasa da na ‘yan sandan Nijeriya zuwa ga zababben shugaban kasa da mataimakinsa.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Da yake magana kan barazanar da wasu ke yi na cewa mika mulki a ranar 29 ga watan Mayu ba za ta tabbata ba, ya ce an samar da dukkan matakan tsaro domin dakile duk masu shirin tayar da fitina, yana mai cewa duk wanda bai gamsu da yadda zaben ya gudana ba, ya kamata su fitar da korafe-korafensu ta hanyar kotu.

Ya ce: “Tsarin mika mulki yana kan gaba kuma da yardar Allah za a mika mulki a ranar 29 ga watan Mayu, lamari ne da ya shafi tsarin mulki, kuma duk wasu kararraki ko an warware ko kuma ba a warware su ba, ba za su hana mika mulki a hukumance ba.

“Shugaba Buhari ba zai kara ko kwana guda ba bayan ranar 29 ga watan Mayu, zai mika wa duk wanda hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana a matsayin zababben shugaban kasa. Kotu za ta ci gaba da gudanar da ayyukanta na yin hukunci na wadannan shari’o’in ko da bayan rantsar da sabon shugaban kasa. Ba wannan ne karon farko da muke gudanar da zabe ba, wannan ba shi ne karon farko da mutane ke karbar mukamai da kararraki ba.

“Batutuwan da ke gaban sauraran kararrakin zabe za su ci gaba da tafiya ba tare da wata matsala ba har sai an yanke hukuncin karshe a kotun koli, kuma bangarorin da abin ya shafa za su gamsu da hukunci a kowane mataki na kararrakin.

“Muna yin komai don ganin cewa tsarin mika mulki bai darkushe ba. Gwamnatin tarayya ta yi wani bayani kan hakan. Jami’an tsaro da wani bangare na masu leken asiri na kwamitin mika mulki na shugaban kasa za su yi duk abin da zai tabbatar da cewa babu abin da ya faru da zai kawo cikas ga tsarin mika mulki cikin lumana,” in ji sakataren gwamnatin tarayya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Atiku Ba Zai Yi Ritaya Daga Siyasa Ba -Dino Melaye

Next Post

INEC: Dauda Lawal Ya Karbi Takardar Shaidar Lashe Zaben Gwamnan Jihar Zamfara

Related

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta
Labarai

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

8 hours ago
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

11 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

11 hours ago
Gwamnatin Tarayya
Labarai

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

13 hours ago
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki
Labarai

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

15 hours ago
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

15 hours ago
Next Post
INEC: Dauda Lawal Ya Karbi Takardar Shaidar Lashe Zaben Gwamnan Jihar Zamfara

INEC: Dauda Lawal Ya Karbi Takardar Shaidar Lashe Zaben Gwamnan Jihar Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Gwamnatin Tarayya

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.