ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wani Abu Da Zai Hana Mika Mulki A Ranar 29 Ga Mayu –Gwamnatin Tarayya

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin tarayya ta gargadi duk masu shirin kawo tarnaki ga tsarin mika mulki da shugaban kasa mai ci Muhammadu Buhari zai yi ga zababben shugaban kasa, Asiwaju Ahmed Bola Tinubu a ranar 29 ga watan Mayu.

Sakataren gwamnatin tarayya, Mista Boss Mustapha shi ya yi wannan gargadin a ranar Talata a Abuja, yayin da yake bayani kan ayyukan kwamitin mika mulki na shugaban kasa, ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa tsarin mika mulki ya kankama, kuma a ranar 29 ga watan Mayu za a mika mulki ga sabon shugaban kasar cikin lumana.

  • Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu

Ya kuma bayyana cewa bayan ayyana Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a matsayin zababben shugaban kasa, kwamitin mika mulki ta bukace shi da ya zabo wakilansa ga majalisar kamar yadda dokar zartarwa ta tanada.

ADVERTISEMENT

Don haka, Mustapha ya ce zababben shugaban kasa ya zabi Atiku Bagudu, Gwamnan Jihar Kebbi da kuma Cif Olawale Edun wadanda tun daga lokacin suka shiga aikin gadan-gadan.

Ya kuma bayyana cewa a yanzu haka zababben shugaban kasa ya tare a gidan tsaro, sannan kuma an tura jami’an tsaro na ma’aikatar harkokin wajen kasa da na ‘yan sandan Nijeriya zuwa ga zababben shugaban kasa da mataimakinsa.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Da yake magana kan barazanar da wasu ke yi na cewa mika mulki a ranar 29 ga watan Mayu ba za ta tabbata ba, ya ce an samar da dukkan matakan tsaro domin dakile duk masu shirin tayar da fitina, yana mai cewa duk wanda bai gamsu da yadda zaben ya gudana ba, ya kamata su fitar da korafe-korafensu ta hanyar kotu.

Ya ce: “Tsarin mika mulki yana kan gaba kuma da yardar Allah za a mika mulki a ranar 29 ga watan Mayu, lamari ne da ya shafi tsarin mulki, kuma duk wasu kararraki ko an warware ko kuma ba a warware su ba, ba za su hana mika mulki a hukumance ba.

“Shugaba Buhari ba zai kara ko kwana guda ba bayan ranar 29 ga watan Mayu, zai mika wa duk wanda hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana a matsayin zababben shugaban kasa. Kotu za ta ci gaba da gudanar da ayyukanta na yin hukunci na wadannan shari’o’in ko da bayan rantsar da sabon shugaban kasa. Ba wannan ne karon farko da muke gudanar da zabe ba, wannan ba shi ne karon farko da mutane ke karbar mukamai da kararraki ba.

“Batutuwan da ke gaban sauraran kararrakin zabe za su ci gaba da tafiya ba tare da wata matsala ba har sai an yanke hukuncin karshe a kotun koli, kuma bangarorin da abin ya shafa za su gamsu da hukunci a kowane mataki na kararrakin.

“Muna yin komai don ganin cewa tsarin mika mulki bai darkushe ba. Gwamnatin tarayya ta yi wani bayani kan hakan. Jami’an tsaro da wani bangare na masu leken asiri na kwamitin mika mulki na shugaban kasa za su yi duk abin da zai tabbatar da cewa babu abin da ya faru da zai kawo cikas ga tsarin mika mulki cikin lumana,” in ji sakataren gwamnatin tarayya.

Gwamnatin Tarayya
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Next Post
INEC: Dauda Lawal Ya Karbi Takardar Shaidar Lashe Zaben Gwamnan Jihar Zamfara

INEC: Dauda Lawal Ya Karbi Takardar Shaidar Lashe Zaben Gwamnan Jihar Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.