ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wani Abu Da Zai Hana Mika Mulki A Ranar 29 Ga Mayu –Gwamnatin Tarayya

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin tarayya ta gargadi duk masu shirin kawo tarnaki ga tsarin mika mulki da shugaban kasa mai ci Muhammadu Buhari zai yi ga zababben shugaban kasa, Asiwaju Ahmed Bola Tinubu a ranar 29 ga watan Mayu.

Sakataren gwamnatin tarayya, Mista Boss Mustapha shi ya yi wannan gargadin a ranar Talata a Abuja, yayin da yake bayani kan ayyukan kwamitin mika mulki na shugaban kasa, ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa tsarin mika mulki ya kankama, kuma a ranar 29 ga watan Mayu za a mika mulki ga sabon shugaban kasar cikin lumana.

  • Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu

Ya kuma bayyana cewa bayan ayyana Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a matsayin zababben shugaban kasa, kwamitin mika mulki ta bukace shi da ya zabo wakilansa ga majalisar kamar yadda dokar zartarwa ta tanada.

ADVERTISEMENT

Don haka, Mustapha ya ce zababben shugaban kasa ya zabi Atiku Bagudu, Gwamnan Jihar Kebbi da kuma Cif Olawale Edun wadanda tun daga lokacin suka shiga aikin gadan-gadan.

Ya kuma bayyana cewa a yanzu haka zababben shugaban kasa ya tare a gidan tsaro, sannan kuma an tura jami’an tsaro na ma’aikatar harkokin wajen kasa da na ‘yan sandan Nijeriya zuwa ga zababben shugaban kasa da mataimakinsa.

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Da yake magana kan barazanar da wasu ke yi na cewa mika mulki a ranar 29 ga watan Mayu ba za ta tabbata ba, ya ce an samar da dukkan matakan tsaro domin dakile duk masu shirin tayar da fitina, yana mai cewa duk wanda bai gamsu da yadda zaben ya gudana ba, ya kamata su fitar da korafe-korafensu ta hanyar kotu.

Ya ce: “Tsarin mika mulki yana kan gaba kuma da yardar Allah za a mika mulki a ranar 29 ga watan Mayu, lamari ne da ya shafi tsarin mulki, kuma duk wasu kararraki ko an warware ko kuma ba a warware su ba, ba za su hana mika mulki a hukumance ba.

“Shugaba Buhari ba zai kara ko kwana guda ba bayan ranar 29 ga watan Mayu, zai mika wa duk wanda hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana a matsayin zababben shugaban kasa. Kotu za ta ci gaba da gudanar da ayyukanta na yin hukunci na wadannan shari’o’in ko da bayan rantsar da sabon shugaban kasa. Ba wannan ne karon farko da muke gudanar da zabe ba, wannan ba shi ne karon farko da mutane ke karbar mukamai da kararraki ba.

“Batutuwan da ke gaban sauraran kararrakin zabe za su ci gaba da tafiya ba tare da wata matsala ba har sai an yanke hukuncin karshe a kotun koli, kuma bangarorin da abin ya shafa za su gamsu da hukunci a kowane mataki na kararrakin.

“Muna yin komai don ganin cewa tsarin mika mulki bai darkushe ba. Gwamnatin tarayya ta yi wani bayani kan hakan. Jami’an tsaro da wani bangare na masu leken asiri na kwamitin mika mulki na shugaban kasa za su yi duk abin da zai tabbatar da cewa babu abin da ya faru da zai kawo cikas ga tsarin mika mulki cikin lumana,” in ji sakataren gwamnatin tarayya.

Gwamnatin Tarayya
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
Next Post
INEC: Dauda Lawal Ya Karbi Takardar Shaidar Lashe Zaben Gwamnan Jihar Zamfara

INEC: Dauda Lawal Ya Karbi Takardar Shaidar Lashe Zaben Gwamnan Jihar Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.