ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wani Abu Da Zai Hana Mika Mulki A Ranar 29 Ga Mayu –Gwamnatin Tarayya

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin tarayya ta gargadi duk masu shirin kawo tarnaki ga tsarin mika mulki da shugaban kasa mai ci Muhammadu Buhari zai yi ga zababben shugaban kasa, Asiwaju Ahmed Bola Tinubu a ranar 29 ga watan Mayu.

Sakataren gwamnatin tarayya, Mista Boss Mustapha shi ya yi wannan gargadin a ranar Talata a Abuja, yayin da yake bayani kan ayyukan kwamitin mika mulki na shugaban kasa, ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa tsarin mika mulki ya kankama, kuma a ranar 29 ga watan Mayu za a mika mulki ga sabon shugaban kasar cikin lumana.

  • Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu

Ya kuma bayyana cewa bayan ayyana Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a matsayin zababben shugaban kasa, kwamitin mika mulki ta bukace shi da ya zabo wakilansa ga majalisar kamar yadda dokar zartarwa ta tanada.

ADVERTISEMENT

Don haka, Mustapha ya ce zababben shugaban kasa ya zabi Atiku Bagudu, Gwamnan Jihar Kebbi da kuma Cif Olawale Edun wadanda tun daga lokacin suka shiga aikin gadan-gadan.

Ya kuma bayyana cewa a yanzu haka zababben shugaban kasa ya tare a gidan tsaro, sannan kuma an tura jami’an tsaro na ma’aikatar harkokin wajen kasa da na ‘yan sandan Nijeriya zuwa ga zababben shugaban kasa da mataimakinsa.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Da yake magana kan barazanar da wasu ke yi na cewa mika mulki a ranar 29 ga watan Mayu ba za ta tabbata ba, ya ce an samar da dukkan matakan tsaro domin dakile duk masu shirin tayar da fitina, yana mai cewa duk wanda bai gamsu da yadda zaben ya gudana ba, ya kamata su fitar da korafe-korafensu ta hanyar kotu.

Ya ce: “Tsarin mika mulki yana kan gaba kuma da yardar Allah za a mika mulki a ranar 29 ga watan Mayu, lamari ne da ya shafi tsarin mulki, kuma duk wasu kararraki ko an warware ko kuma ba a warware su ba, ba za su hana mika mulki a hukumance ba.

“Shugaba Buhari ba zai kara ko kwana guda ba bayan ranar 29 ga watan Mayu, zai mika wa duk wanda hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana a matsayin zababben shugaban kasa. Kotu za ta ci gaba da gudanar da ayyukanta na yin hukunci na wadannan shari’o’in ko da bayan rantsar da sabon shugaban kasa. Ba wannan ne karon farko da muke gudanar da zabe ba, wannan ba shi ne karon farko da mutane ke karbar mukamai da kararraki ba.

“Batutuwan da ke gaban sauraran kararrakin zabe za su ci gaba da tafiya ba tare da wata matsala ba har sai an yanke hukuncin karshe a kotun koli, kuma bangarorin da abin ya shafa za su gamsu da hukunci a kowane mataki na kararrakin.

“Muna yin komai don ganin cewa tsarin mika mulki bai darkushe ba. Gwamnatin tarayya ta yi wani bayani kan hakan. Jami’an tsaro da wani bangare na masu leken asiri na kwamitin mika mulki na shugaban kasa za su yi duk abin da zai tabbatar da cewa babu abin da ya faru da zai kawo cikas ga tsarin mika mulki cikin lumana,” in ji sakataren gwamnatin tarayya.

Gwamnatin Tarayya
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
INEC: Dauda Lawal Ya Karbi Takardar Shaidar Lashe Zaben Gwamnan Jihar Zamfara

INEC: Dauda Lawal Ya Karbi Takardar Shaidar Lashe Zaben Gwamnan Jihar Zamfara

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.