• English
  • Business News
Friday, May 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa babu wani shirin kwaso ‘yan Nijeriya daga kasar Israila ko kuma Falasdin, domin babu wanda ya bukaci hakan.

Ma’aikatar kula da ‘yan Nijeriya da ke kasashen ketare (NiDCOM), ita ce ta bayyana hakan, inda ta ce ba ta samu wani kiran waya ba daga wani mutum ko kungiya na ‘yan Nijeriya da ke cikin barazana ba game da yakin da ya barke tsakanin Isra’ila da Falasdinawa.

  • Gobe Za A Tsame Duk Ma’aikacin Tarayya Da Ba Ya Cikin Tsarin IPPIS Daga Biyan Albashi
  • Xi Jinping Ya Gana Da Gwamnan Jihar California Dake Amurka

NIDCOM ta kara da cewa za ta kwaso ‘yan Nijeriya ne kawai idan ta samu kiran waya daga ‘yan Nijeriyan da ke kasashen guda biyu, amma har yanzu ba ta samu hakan ba.

Mai magana da yawun ma’aikatan, Abdur-Rahman Balogun shi ya bayyana hakan lokacin da yake zantawa da kamfanin dallancin labarai na Nijeriya (NAN) a Abuja.

Balogun yana mayar da martani ne ga wata tambaya kan ko me gwamnatin tarayya ke yi na kwashe ‘yan Nijeriya mazauna yankunan da ake gwabzawa fada a gabas ta tsakiya.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

Mayar Da Hankali A Aikin Farfado Da Kwararrun Asibitocin Gwamnatin Tarayyya

Dubban ‘yan kasashen waje ne suka makale a Isra’ila da kuma kasar Falasdin, inda ake gwabza kazamin yaki tun bayan da kungiyar Hamas ta kaddamar da hari.

Rikicin ya yi sanadin mutuwar dubban mutane daga bangarorin biyu, kasashe da dama sun kaddamar da ayyukan kwashe ‘yan kasarsu zuwa gida, yayin da wasu ke shirin yin hakan.

Ya zuwa yanzu dai kasashe irinsu Amurka da Jamus da Ukraine da Thailand da Koriya ta Kudu da Austiriya da Brazil da kuma Argentina na daga cikin kasashen da suka mayar da ‘yan kasarsu gida.

Mai magana da yawun NiDCOM ya ce ‘yan wasu kasashe sun yi kiran gaggawa ga gwamnatocinsu na gida don neman taimako, “amma ba mu samu ko kira daya daga ‘yan kasarmu da ke yankunan guda biyu ba.”

Ya tunatar da cewa Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, ya fitar da wata sanarwa, inda ya ce ’yan Nijeriya mazauna kasashen waje ba sa fuskantar matsin lamba saboda yakin da ake yi a zirin Gaza.

A cewarsa, ma’aikatar za ta iya yin aiki ne kawai idan ta sami kiran gaggawa daga mutanen da ke cikin kasashe masu fama da rikici.

Ya kara da cewa a lokacin da NiDCOM da sauran hukumomin da abin ya shafab a kasar suka samu kiran gaggawa daga ‘yan Nijeriya mazauna kasar Sin, a lokacin barkewar cutar Korona, da kuma na yakin Ukraine da Sudan lokacin da yakin ya barke a yankunan, “mun amsa kuma da yawa daga cikin ‘yan kasarmu mun mayar da su gida.”

Sojojin Isra’ila sun umurci sama da mutane miliyan daya da su fice daga arewacin Gaza cikin sa’o’i 24 gabanin wani samame da sojoji ke shirin kaiwa.

Kusan ‘yan Falasdin 5,100 ne aka kashe a Zirin Gaza tun bayan da Isra’ila ta kaddamar da hare-haren bama-bamai a yankin da ta mamaye bayan harin da Hamas ta kai a cikin Isra’ila fiye da makonni biyu da suka wuce.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fatattakar Gaza: Ya Kamata Duniya Ta Yi Mana Adalci – Jakadan Falasdin A Nijeriya

Next Post

GORON JUMA’A

Related

Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta
Manyan Labarai

Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

14 hours ago
Mayar Da Hankali A Aikin Farfado Da Kwararrun Asibitocin Gwamnatin Tarayyya
Manyan Labarai

Mayar Da Hankali A Aikin Farfado Da Kwararrun Asibitocin Gwamnatin Tarayyya

15 hours ago
Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 
Manyan Labarai

Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

1 day ago
Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur
Manyan Labarai

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur

1 day ago
Tsaro Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Bunƙasa Tattalin Arziƙi – Atiku
Manyan Labarai

Tsaro Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Bunƙasa Tattalin Arziƙi – Atiku

1 day ago
‘Yan Majalisar Dokokin Nijeriya Sun Bukaci Karin Albashi
Manyan Labarai

Yadda ‘Yan Majalisa Ke Cusa Ayyuka Marasa Amfani A Kasafin Kuɗi – Rahoto

2 days ago
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA'A

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

May 23, 2025
Sin Da ASEAN Sun Kammala Tattaunawa Game Da Kafa Yankin Ciniki Cikin ‘Yanci

Sin Da ASEAN Sun Kammala Tattaunawa Game Da Kafa Yankin Ciniki Cikin ‘Yanci

May 23, 2025
An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing

May 23, 2025
Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

May 23, 2025
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

May 23, 2025

Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

May 23, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz

May 23, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

May 23, 2025
Shugaban Kasar Sin Ya Jaddada Muhimmancin Samun Ci Gaba Mai Inganci Ta Fuskar Raya Wayewar Kai

Shugaban Kasar Sin Ya Jaddada Muhimmancin Samun Ci Gaba Mai Inganci Ta Fuskar Raya Wayewar Kai

May 23, 2025
Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

May 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.