• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wata Kasa Da Za Ta Ce ”Ita Kadai Ta Isa Gayya”

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Babu Wata Kasa Da Za Ta Ce ”Ita Kadai Ta Isa Gayya”
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An yi zama na II na taron kungiyar G20 karo na 19 a jiya Litinin, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da jawabi mai taken ”Hada Hannu Domin Tafiyar da Tsarin Tattalin Arzikin Duniya Bisa Adalci da Daidaito”. 

 

A ra’ayina, wannan jawabi ya gabatar da shawarwari da hanya mai sauki ta shawo kan matsalolin tattalin arziki da duniya ke fama da su, har ma da hanyoyin da kasashe za su iya hada hannu domin taimakon juna.

  • Sin Da Afirka Na Da Buri Daya A Wajen Taron G20
  • Shugaba Xi Jinping Ya Ce Kasar Sin Da Birtaniya Na Da Dimbin Sararin Yin Hadin Gwiwa

Daga cikin kalaman shugaba Xi, akwai wadanda suka fi jan hankalina, inda yake cewa, ya kamata a yi adawa da kariyar cinikayya da ra’ayin bangare daya da sanya yarjejeniyar saukaka zuba jari domin samun ci gaba, cikin tsarin dokokin WTO.

 

Labarai Masu Nasaba

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Zan iya cewa, cikin wadannan kalamai kalilan, shugaban ya gabatar da mafita mafi sauki ga matsalolin duniya. Idan muka dauki batun kariyar cinikayya da zartar da ra’ayin bangare guda da wasu kasashen duniya ke ganin su ne mafita gare su, mun riga mun ga yadda hakan bai amfanawa kowannne bangare da komai ba. Ci gaban wata kasa, dama ce ga sauran kasashen duniya maimakon barazana ko kalubale. Mun riga mun gane cewa, babu wata kasa da za ta iya cewa za ta raba gari da wata, domin makomar kasashen na hade da juna. Idan wata na fama da talauci ko matsaloli, to wadannan matsaloli na iya bazuwa ga sauran, haka ma idan tana cikin wadata da kwanciyar hankali. Idan muka dauki Sin a matsayin misali, muhimmiyar rawar da take takawa wajen samarwa duniya damarmaki da dimbin gudunmuwarta ga ci gaban tattalin arzikin duniya, abu ne da ba zai misaltu ba, don haka, babu wata kasa da za ta ce ta yanke mu’amala da ita ko kuma ta bugi kirjin cewa ita kadai (kasar) ta isa gayya.

 

Idan har ba neman fifiko ko mulkin danniya ba, to mene ne dalilin wariya ko kariyar cinikayya tsakanin kasashe bayan mafita ita ce hada hannu tsakaninsu domin cin moriyar juna? A wannan zamani da ake ciki, ba zai yuwu duniya ta ci gaba da kasancewa karkashin ikon wata kasa daya ko wasu kasashe kalilan ba, dole ne irin wadannan kasashe su zubar da girman kai su hada kai da sauran takwarorinsu domin ceto duniya daga fadawa mummunan yanayi. (Fa’iza Musatapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Da Afirka Na Da Buri Daya A Wajen Taron G20

Next Post

Kwalara Ta Yi Ajalin Mutane 25 A Sakkwato

Related

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

11 hours ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

12 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

13 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

14 hours ago
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka
Daga Birnin Sin

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

15 hours ago
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154
Daga Birnin Sin

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

16 hours ago
Next Post
Kwalara Ta Yi Ajalin Mutane 25 A Sakkwato

Kwalara Ta Yi Ajalin Mutane 25 A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.