• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Badakala A Kano: An Gano Biliyan 4 Da Ta Yi Batan-Dabo A KASCO

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Badakala A Kano: An Gano Biliyan 4 Da Ta Yi Batan-Dabo A KASCO
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Karbar Koke-Koke da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano (PCACC), ta cafke ma’aikata takwas na kamfanin samar samar da kayan noma (KASCO) kan zargin almundahanar sama da Naira biliyan 4.3 a shekara guda. 

Kazalika, hukumar ta kwace kadarori da suka hada har da rumbun adana kayan noma guda takwas da ke dauke da motoci, tiraktoci, dubban buhunan taki, waken suya, siminti, dawa, da wasu da dama da ake zargin an saye su da lalitar gwamnati.

  • ’Yan Bindiga Sun Kashe Shugaban JIBWIS, Sun Sace Mutane 50 A Kaduna
  • Yau Real Madrid Da Barcelona Za Su Barje Gumi

Shugaban hukumar, Muhyi Magaji Rimin Gado, ya bayyana haka a ranar Asabar.

Ya ce kadarorin da aka kwato a karamar hukumar Kubmotso, bincike ya nuna cewa an yi amfani da wasu kamfanoni wajen yin da zambar.

“Wannan kamfanin Association of Compassionate Friends an yi masa rijista a 2019 da manufar taimakawa da rage barace-barace ga yara, shi kuma kamfanin Limestone Processing Links an mawa rijista ya samu miliyan 480.”

Labarai Masu Nasaba

Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

Ya ce kadarar an kwace ta tare da mika ta ga ‘yansanda bayan samun umarni daga kotu.

A umarnin kotun, akwai sunan manajan kamfanin KASCO, Bala Inuwa Muhammad, da aka ce ba a san inda yake ba a halin yanzu a matsayin wanda ake zargi na farko a cikin mutum tara da suka hada da Najib Muhammad, Abdullahi Ibrahim, Aminu Sadiq, Umar Alhassan, Surajo Lawal, Safiyanu Tsakuwa, Nura Yusuf da Aminu Fagge Lawal.

Wata majiya ta ce, kamfanin KASCO daga ranar 19 ga watan Agustan, 2022 zuwa 3 ga Afrilun 2023, ya biya kamfanin Association of Compassionate Friends kudi har naira biliyan 3.2 a lokuta daban-daban har 12 da kuma miliyan N480 da aka biya kamfanin Limestone Processing Links a karo biyu.

“Mun tabbatar an biya miliyan 20, miliyan 30 da miliyan 78.6 zuwa asusun masu zaman kansu da wata gidauniya daya,” cewar masu bincike.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Badakalae KudiHukumar Yaki Da Cin Hanci Da RashawaKASCOMuhyi Magaji Rimin Gado
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ina Dalilin Da Ya Sa Amurka Ta Hura Wutar Rikici Game Da “Yin Takara A Sararin Samaniya” Tare Da Kasar Sin A Argentina?

Next Post

Wakilin Sin A MDD Ya Yi Kira Da A Dagewa Wasu Kasashen Afirka Takunkumai

Related

Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya
Labarai

Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

2 hours ago
Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa
Labarai

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

3 hours ago
Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

4 hours ago
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku
Labarai

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

5 hours ago
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 
Labarai

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

5 hours ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

9 hours ago
Next Post
Wakilin Sin A MDD Ya Yi Kira Da A Dagewa Wasu Kasashen Afirka Takunkumai

Wakilin Sin A MDD Ya Yi Kira Da A Dagewa Wasu Kasashen Afirka Takunkumai

LABARAI MASU NASABA

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

October 5, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

October 5, 2025
Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

October 5, 2025
Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

October 5, 2025
Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.