• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Badakala A Kano: An Gano Biliyan 4 Da Ta Yi Batan-Dabo A KASCO

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Kano

Hukumar Karbar Koke-Koke da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano (PCACC), ta cafke ma’aikata takwas na kamfanin samar samar da kayan noma (KASCO) kan zargin almundahanar sama da Naira biliyan 4.3 a shekara guda. 

Kazalika, hukumar ta kwace kadarori da suka hada har da rumbun adana kayan noma guda takwas da ke dauke da motoci, tiraktoci, dubban buhunan taki, waken suya, siminti, dawa, da wasu da dama da ake zargin an saye su da lalitar gwamnati.

  • ’Yan Bindiga Sun Kashe Shugaban JIBWIS, Sun Sace Mutane 50 A Kaduna
  • Yau Real Madrid Da Barcelona Za Su Barje Gumi

Shugaban hukumar, Muhyi Magaji Rimin Gado, ya bayyana haka a ranar Asabar.

Ya ce kadarorin da aka kwato a karamar hukumar Kubmotso, bincike ya nuna cewa an yi amfani da wasu kamfanoni wajen yin da zambar.

“Wannan kamfanin Association of Compassionate Friends an yi masa rijista a 2019 da manufar taimakawa da rage barace-barace ga yara, shi kuma kamfanin Limestone Processing Links an mawa rijista ya samu miliyan 480.”

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

Ya ce kadarar an kwace ta tare da mika ta ga ‘yansanda bayan samun umarni daga kotu.

A umarnin kotun, akwai sunan manajan kamfanin KASCO, Bala Inuwa Muhammad, da aka ce ba a san inda yake ba a halin yanzu a matsayin wanda ake zargi na farko a cikin mutum tara da suka hada da Najib Muhammad, Abdullahi Ibrahim, Aminu Sadiq, Umar Alhassan, Surajo Lawal, Safiyanu Tsakuwa, Nura Yusuf da Aminu Fagge Lawal.

Wata majiya ta ce, kamfanin KASCO daga ranar 19 ga watan Agustan, 2022 zuwa 3 ga Afrilun 2023, ya biya kamfanin Association of Compassionate Friends kudi har naira biliyan 3.2 a lokuta daban-daban har 12 da kuma miliyan N480 da aka biya kamfanin Limestone Processing Links a karo biyu.

“Mun tabbatar an biya miliyan 20, miliyan 30 da miliyan 78.6 zuwa asusun masu zaman kansu da wata gidauniya daya,” cewar masu bincike.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
Labarai

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Next Post
Wakilin Sin A MDD Ya Yi Kira Da A Dagewa Wasu Kasashen Afirka Takunkumai

Wakilin Sin A MDD Ya Yi Kira Da A Dagewa Wasu Kasashen Afirka Takunkumai

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.