ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Dace Takara Ta Zamo Kalmar Kwatanta Alakar Sin Da Amurka Ba

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

A shekarun baya bayan nan, mahukuntan kasar Amurka na yawaita jaddada kalmar Takara, a lokutan da suke tattauna batun alakar kasar su da Sin, har ma wannan kalma na neman zama tamkar ita ce Jigon” cudanyar sassan biyu.

Matakai daban daban da gwamnatin Amurka ke dauka, sun bayyana a fili yadda wannan kalma ta “Takara” ta shiga bakin kusoshin gwamnatin kasar, inda take wakiltar matakan nuna fin karfi, da kokarin dakile ci gaban Sin, da ma yiwa Sin din matsin lamba ta fannoni mabanbanta.

  • Shugaba Xi Jinping Da Takwaransa Na Afirka Ta Kudu Sun Jagoranci Taron Tattaunawa A Tsakanin Shugabannin Sin Da Afirka

To sai idan mun lura da matsayin kasashen biyu, abu ne mai kyau su yi takara mai tsafta a bangarori irin su cinikayya da raya fasahohi. Irin wadannan matakai na takara, ya dace su zamo bisa adalci, da kuma sanin ya kamata, kuma ya wajaba a gudanar da su kan tsari bisa dokoki tabbatattu.

ADVERTISEMENT

Kaza lika, bai dace su zama matakai na watsi da dokokin raya tattalin arziki, da kuma sharuddan cudanyar sassan kasa da kasa ba. Har ila yau, bai dace a yi amfani da irin wadannan matakai wajen murgunawa wasu sassa ba.

Mun ga misalai da dama, dake nuna yadda Amurka karkashin manufar takara, take amfani da karfin ikonta wajen dakile ci gaban wasu kasashe, tare da salwantar da moriyar wasu kasashen, domin cimma nasarar takarar da ta sanya gaba. Hakika wannan dabara ta sabawa ainihin maanar takara mai kyau, maimakon haka, manufofi ne masu alaka da In ban samu ba, to kowa ya rasa da tunani irin na cacar baka.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Sau da dama, mummunar takara daga bangaren Amurka na harzuka bangaren Sin, tare da lahanta moriyar kasar, da sukar manufofin ta musamman ta fuskar siyasa, da ikon mulkin kai, wanda hakan ya yi matukar keta hurumin kaidojin dangantakar kasa da kasa, da lahanta ginshikin cudanya a fannin siyasa tsakanin sassan biyu.

Don haka dai a takaice, maimakon ingiza matakan fito na fito, da rura wutar sabani da wariya, kamata ya yi sassan biyu su mayar da hankali ga bunkasa matakan cimma moriyar juna, da kyautata mutuntaka, da gudanar da takara a fannin inganta jagorancin alumma, da kiyaye moriyar ’yan kasa.

A matsayin Amurka da Sin na kasashe masu karfin tattalin arziki, kamata ya yi takararsu ta karkata ga nunawa duniya kyakkyawan misali, na yadda suke sauke nauyin bunkasa rayuwar alummunsu, da farfado da ci gaba bayan annoba, da shawo kan kalubalen sauyin yanayi, da matsalolin yankunansu, da kare kyakkyawan yanayin muhallin duniya, da wanzar da zaman lafiya, da samar da wadata ga alummun duniya kusan biliyan 8, ciki har da Sinawa da Amurkawa. (Saminu Alhassan)

 

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Sin Da Kasashe Masu Ra’ayi Iri Daya Sun Yi Kira Da A Inganta Rayuwar Mata Masu Bukata Ta Musamman A Cikin Al’umma

Sin Da Kasashe Masu Ra’ayi Iri Daya Sun Yi Kira Da A Inganta Rayuwar Mata Masu Bukata Ta Musamman A Cikin Al’umma

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.