ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Dace Takara Ta Zamo Kalmar Kwatanta Alakar Sin Da Amurka Ba

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

A shekarun baya bayan nan, mahukuntan kasar Amurka na yawaita jaddada kalmar Takara, a lokutan da suke tattauna batun alakar kasar su da Sin, har ma wannan kalma na neman zama tamkar ita ce Jigon” cudanyar sassan biyu.

Matakai daban daban da gwamnatin Amurka ke dauka, sun bayyana a fili yadda wannan kalma ta “Takara” ta shiga bakin kusoshin gwamnatin kasar, inda take wakiltar matakan nuna fin karfi, da kokarin dakile ci gaban Sin, da ma yiwa Sin din matsin lamba ta fannoni mabanbanta.

  • Shugaba Xi Jinping Da Takwaransa Na Afirka Ta Kudu Sun Jagoranci Taron Tattaunawa A Tsakanin Shugabannin Sin Da Afirka

To sai idan mun lura da matsayin kasashen biyu, abu ne mai kyau su yi takara mai tsafta a bangarori irin su cinikayya da raya fasahohi. Irin wadannan matakai na takara, ya dace su zamo bisa adalci, da kuma sanin ya kamata, kuma ya wajaba a gudanar da su kan tsari bisa dokoki tabbatattu.

ADVERTISEMENT

Kaza lika, bai dace su zama matakai na watsi da dokokin raya tattalin arziki, da kuma sharuddan cudanyar sassan kasa da kasa ba. Har ila yau, bai dace a yi amfani da irin wadannan matakai wajen murgunawa wasu sassa ba.

Mun ga misalai da dama, dake nuna yadda Amurka karkashin manufar takara, take amfani da karfin ikonta wajen dakile ci gaban wasu kasashe, tare da salwantar da moriyar wasu kasashen, domin cimma nasarar takarar da ta sanya gaba. Hakika wannan dabara ta sabawa ainihin maanar takara mai kyau, maimakon haka, manufofi ne masu alaka da In ban samu ba, to kowa ya rasa da tunani irin na cacar baka.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 8 Zuwa Sararin Samaniya

Mujallar Qiushi Za Ta Buga Muhimmin Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Ciyar Da Ilimi, Fasaha Da Kwararru Gaba Tare”

Sau da dama, mummunar takara daga bangaren Amurka na harzuka bangaren Sin, tare da lahanta moriyar kasar, da sukar manufofin ta musamman ta fuskar siyasa, da ikon mulkin kai, wanda hakan ya yi matukar keta hurumin kaidojin dangantakar kasa da kasa, da lahanta ginshikin cudanya a fannin siyasa tsakanin sassan biyu.

Don haka dai a takaice, maimakon ingiza matakan fito na fito, da rura wutar sabani da wariya, kamata ya yi sassan biyu su mayar da hankali ga bunkasa matakan cimma moriyar juna, da kyautata mutuntaka, da gudanar da takara a fannin inganta jagorancin alumma, da kiyaye moriyar ’yan kasa.

A matsayin Amurka da Sin na kasashe masu karfin tattalin arziki, kamata ya yi takararsu ta karkata ga nunawa duniya kyakkyawan misali, na yadda suke sauke nauyin bunkasa rayuwar alummunsu, da farfado da ci gaba bayan annoba, da shawo kan kalubalen sauyin yanayi, da matsalolin yankunansu, da kare kyakkyawan yanayin muhallin duniya, da wanzar da zaman lafiya, da samar da wadata ga alummun duniya kusan biliyan 8, ciki har da Sinawa da Amurkawa. (Saminu Alhassan)

 

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 8 Zuwa Sararin Samaniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 8 Zuwa Sararin Samaniya

June 15, 2026
Mujallar Qiushi Za Ta Buga Muhimmin Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Ciyar Da Ilimi, Fasaha Da Kwararru Gaba Tare”
Daga Birnin Sin

Mujallar Qiushi Za Ta Buga Muhimmin Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Ciyar Da Ilimi, Fasaha Da Kwararru Gaba Tare”

June 15, 2026
Dunkulewar Kasa Shi Ne Burin Bai Daya Na Jama’ar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan
Daga Birnin Sin

Dunkulewar Kasa Shi Ne Burin Bai Daya Na Jama’ar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan

June 15, 2026
Next Post
Sin Da Kasashe Masu Ra’ayi Iri Daya Sun Yi Kira Da A Inganta Rayuwar Mata Masu Bukata Ta Musamman A Cikin Al’umma

Sin Da Kasashe Masu Ra’ayi Iri Daya Sun Yi Kira Da A Inganta Rayuwar Mata Masu Bukata Ta Musamman A Cikin Al’umma

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Kwamishinan ‘Yansandan Legas, Khan Salihu, Ya Rasu

Mataimakin Kwamishinan ‘Yansandan Legas, Khan Salihu, Ya Rasu

June 16, 2026
Hauhawar Farashi Ya Kai Kashi 15.93 Cikin 1000 A Watan Mayu A Nijeriya – NBS

Hauhawar Farashi Ya Kai Kashi 15.93 Cikin 1000 A Watan Mayu A Nijeriya – NBS

June 16, 2026
Sojoji Sun Ceto Matar Tsohon Kakakin Hedikwatar Tsaro A Katsina

Sojoji Sun Ceto Matar Tsohon Kakakin Hedikwatar Tsaro A Katsina

June 16, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Hukuncin Kotu Kan Ba Da Umarnin Soke Rajistar ADC

June 16, 2026
Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 8 Zuwa Sararin Samaniya

Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 8 Zuwa Sararin Samaniya

June 15, 2026
Mujallar Qiushi Za Ta Buga Muhimmin Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Ciyar Da Ilimi, Fasaha Da Kwararru Gaba Tare”

Mujallar Qiushi Za Ta Buga Muhimmin Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Ciyar Da Ilimi, Fasaha Da Kwararru Gaba Tare”

June 15, 2026
Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

June 15, 2026
Ɗan Kwankwaso Ya Zama Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan NDC A Zaɓen Kano na 2027

Ɗan Kwankwaso Ya Zama Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan NDC A Zaɓen Kano na 2027

June 15, 2026
2023: Tinubu Ya Zaɓi Kashim Shettima A Matsayin Mataimaki

Shin Har Yanzu Shettima Ne Abokin Takarar Tinubu?

June 15, 2026
Dunkulewar Kasa Shi Ne Burin Bai Daya Na Jama’ar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan

Dunkulewar Kasa Shi Ne Burin Bai Daya Na Jama’ar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan

June 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.