• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Kamata Kungiyar EU Ta Biyewa Masu Burin Rusha Alakarta Da Sin Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Bai Kamata Kungiyar EU Ta Biyewa Masu Burin Rusha Alakarta Da Sin Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Na san da yawa cikin masu bibiyar alamuran dake faruwa a harkokin kasa da kasa, ba su manta da yadda a baya bayan nan kungiyar tarayyar Turai EU, ta fitar da wasu sabbin matakai na kakabawa wasu sassan kasar Sin takunkumi ba.

Wato dai batun nan na yadda a farkon makon nan kungiyar EU ta amince da wasu tanade-tanade na kakabawa wasu sassa 84, da daidaikun mutane na wasu kasashe daban daban takunkumai, bisa zarfin wai suna taimakawa dakarun sojin Rasha da kayayyakin aiki, irin su sassan jirage marasa matuka, da sauran abubuwan harhada naurorin laturoni a rikicinta da Ukraine. Kuma 7 daga cikin wadancan sassa da takunkuman suka shafa sun fito ne daga kasar Sin.

  • Sin Da Amurka Za Su Iya Samar Da Alfanu Ga Duniya a Hadin Gwiwarsu
  • Da Rancen Naira Tiriliyan 13 Za A Cike Gibin Kasafin Kudin 2025 — Edun

Ba dai wannan ne karon farko da EU ta dauki irin wannan mataki kan wasu sassa ciki har da daidaikun Sinawa ba, kuma a lokuta daban daban, irin wannan mataki kan hada da takunkumin hana tafiye-tafiye, da daskarar da kadarori, da hana damar samar da kudade, matakan da a baya EUn kan ce na shawo kan kalubalen fitar da hajoji ne.

Illar wannan mataki na EU, shi ne tarayyar Turai na aikewa da wani sako mai karfi ga bangaren Sin, cewa kungiyar na zargin Sin da goyon bayan Rasha a rikicinta da Ukraine, duk da sanin cewa wannan zargi ba gaskiya ba ne, kuma mataki ne da ka iya lahanta alakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin EU da Sin.

Wani abun lura ma shi ne duk da cewa Amurka ta sha kakkaba wasu takunkumai kan kasar Sin, bisa zarginta da goyon bayan Rasha a rikicinta da Ukraine, takunkuman da kuma suka fi tsauri sama da na EU, ba su sauya matsayar Sin na tsayawa bisa adalci, da kin goyon bayan wani bangare a rikicin bana, don haka ya kamata ita ma EU ta san cewa, Sin ba za ta yi watsi da sahihiyar manufarta ta kin goyon bayan rikici da ingiza sulhu ba. Kuma hakan ba ya nuna cewa Sin za ta yi watsi da gudanar da hada-hadar tattalin arziki da cinikayya tsakaninta da kasar Rasha kamar yadda aka saba tun tuni ba.

Labarai Masu Nasaba

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

A wannan gaba da alkaluma ke nuna yawan takunkuman da EU ta kakkabawa kasar Rasha ma sun kai zagaye na 15, ya dace EU ta lura cewa, ba za a iya warware rikicin Rasha da Ukraine ta hanyar kakkaba takunkumai ba, kuma Amurka ce ke da alhakin ingiza wutar rikicin da ya ki ci ya ki cinyewa tsakanin Rasha da Ukraine, da ma makamancinsa na Israila da Hamas a Gaza. Don haka, idan har neman wanda za a dorawa alhakin tashe-tashen hankula dake wakana a Turai da Gabas ta tsakiya ake yi, ya wajaba EU ta mayar da hankali ga Amurka, domin jin bahasi, muddin dai ana son tafiya bisa turbar gaskiya da adalci.(Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Kasa A 2027: Dan Takara Mai Nagarta Kawai Nijeriya Ke Bukata – Shekarau

Next Post

PRP Ta Tabbatar Da Tattaunawar Hadewa Da Jam’iyyar ADC Gabanin Zaben 2027

Related

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

12 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

12 hours ago
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping
Daga Birnin Sin

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

13 hours ago
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

14 hours ago
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

15 hours ago
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

16 hours ago
Next Post
PRP

PRP Ta Tabbatar Da Tattaunawar Hadewa Da Jam’iyyar ADC Gabanin Zaben 2027

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

September 6, 2025
Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya BuÆ™aci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya BuÆ™aci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

September 6, 2025
Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu RiÆ™e Wa Minista Tijjani MuÆ™aminsa Bayan HamÉ“arar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.