• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Kamata Kungiyar EU Ta Biyewa Masu Burin Rusha Alakarta Da Sin Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Bai Kamata Kungiyar EU Ta Biyewa Masu Burin Rusha Alakarta Da Sin Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Na san da yawa cikin masu bibiyar alamuran dake faruwa a harkokin kasa da kasa, ba su manta da yadda a baya bayan nan kungiyar tarayyar Turai EU, ta fitar da wasu sabbin matakai na kakabawa wasu sassan kasar Sin takunkumi ba.

Wato dai batun nan na yadda a farkon makon nan kungiyar EU ta amince da wasu tanade-tanade na kakabawa wasu sassa 84, da daidaikun mutane na wasu kasashe daban daban takunkumai, bisa zarfin wai suna taimakawa dakarun sojin Rasha da kayayyakin aiki, irin su sassan jirage marasa matuka, da sauran abubuwan harhada naurorin laturoni a rikicinta da Ukraine. Kuma 7 daga cikin wadancan sassa da takunkuman suka shafa sun fito ne daga kasar Sin.

  • Sin Da Amurka Za Su Iya Samar Da Alfanu Ga Duniya a Hadin Gwiwarsu
  • Da Rancen Naira Tiriliyan 13 Za A Cike Gibin Kasafin Kudin 2025 — Edun

Ba dai wannan ne karon farko da EU ta dauki irin wannan mataki kan wasu sassa ciki har da daidaikun Sinawa ba, kuma a lokuta daban daban, irin wannan mataki kan hada da takunkumin hana tafiye-tafiye, da daskarar da kadarori, da hana damar samar da kudade, matakan da a baya EUn kan ce na shawo kan kalubalen fitar da hajoji ne.

Illar wannan mataki na EU, shi ne tarayyar Turai na aikewa da wani sako mai karfi ga bangaren Sin, cewa kungiyar na zargin Sin da goyon bayan Rasha a rikicinta da Ukraine, duk da sanin cewa wannan zargi ba gaskiya ba ne, kuma mataki ne da ka iya lahanta alakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin EU da Sin.

Wani abun lura ma shi ne duk da cewa Amurka ta sha kakkaba wasu takunkumai kan kasar Sin, bisa zarginta da goyon bayan Rasha a rikicinta da Ukraine, takunkuman da kuma suka fi tsauri sama da na EU, ba su sauya matsayar Sin na tsayawa bisa adalci, da kin goyon bayan wani bangare a rikicin bana, don haka ya kamata ita ma EU ta san cewa, Sin ba za ta yi watsi da sahihiyar manufarta ta kin goyon bayan rikici da ingiza sulhu ba. Kuma hakan ba ya nuna cewa Sin za ta yi watsi da gudanar da hada-hadar tattalin arziki da cinikayya tsakaninta da kasar Rasha kamar yadda aka saba tun tuni ba.

Labarai Masu Nasaba

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

A wannan gaba da alkaluma ke nuna yawan takunkuman da EU ta kakkabawa kasar Rasha ma sun kai zagaye na 15, ya dace EU ta lura cewa, ba za a iya warware rikicin Rasha da Ukraine ta hanyar kakkaba takunkumai ba, kuma Amurka ce ke da alhakin ingiza wutar rikicin da ya ki ci ya ki cinyewa tsakanin Rasha da Ukraine, da ma makamancinsa na Israila da Hamas a Gaza. Don haka, idan har neman wanda za a dorawa alhakin tashe-tashen hankula dake wakana a Turai da Gabas ta tsakiya ake yi, ya wajaba EU ta mayar da hankali ga Amurka, domin jin bahasi, muddin dai ana son tafiya bisa turbar gaskiya da adalci.(Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Kasa A 2027: Dan Takara Mai Nagarta Kawai Nijeriya Ke Bukata – Shekarau

Next Post

PRP Ta Tabbatar Da Tattaunawar Hadewa Da Jam’iyyar ADC Gabanin Zaben 2027

Related

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?
Daga Birnin Sin

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

4 hours ago
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

6 hours ago
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba
Daga Birnin Sin

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

7 hours ago
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu
Daga Birnin Sin

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

10 hours ago
Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin

17 hours ago
Xi Jinping Zai Halarci Bikin Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan Da Yakin Kin Tafarkin Murdiya
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Bikin Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan Da Yakin Kin Tafarkin Murdiya

18 hours ago
Next Post
PRP

PRP Ta Tabbatar Da Tattaunawar Hadewa Da Jam’iyyar ADC Gabanin Zaben 2027

LABARAI MASU NASABA

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

June 24, 2025
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

June 24, 2025
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

June 24, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

June 24, 2025
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.