ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PRP Ta Tabbatar Da Tattaunawar Hadewa Da Jam’iyyar ADC Gabanin Zaben 2027

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
1 year ago
PRP

Jam’iyyar PRP ta tabbatar da cewa ta fara tattaunawa da wata jam’iyyar adawa ta ADC, kan yuwuwar hadewar jam’iyyun gabanin babban zaben shekarar 2027.

Shugaban jam’iyyar PRP na kasa, Falalu Bello ne ya bayyana hakan a wani taron hadin gwiwa da takwaransa na ADC, Ralph Nwosu a Abuja.

  • Da Rancen Naira Tiriliyan 13 Za A Cike Gibin Kasafin Kudin 2025 — Edun
  • Kisan Jami’an ‘Yansanda 229 A Cikin Wata 22 Babbar Musiba Ce Ga Kasa

Matakin na zuwa ne kwanaki uku bayan da jam’iyyar APC mai mulki ta yi gargadin cewa babu wani hadewar shugabannin ‘yan adawa da suka hada da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da tsohon gwamnan Anambra, Peter Obi, da zai iya kwace kujerar Shugaban kasa Bola Tinubu a zaben 2027.

ADVERTISEMENT

Jam’iyyar APC na mayar da martani ne kan kalaman da mai magana da yawun Atiku, Paul Ibe, ya yi cewa shugaban nasa da takwaransa na jam’iyyar LP duk sun koyi darasi a zaben da ya gabata, kuma za su hada kai domin korar jam’iyya APC a kan karagar mulki.

Haka zalika, wasu jam’iyyun siyasa na adawa a karkashin inuwar hadakar jam’iyyun siyasa da jam’iyyar SDP, su ma sun bayyana shirinsu na tattaunawa kan yiwuwar yin kawance, suna masu cewa kasar na bukatar hadakar Atiku da Obi.

LABARAI MASU NASABA

Ilimi Ne Babban Makamin Daƙile Ta’addanci — Ministan Tsaro

Gwamnatin Borno Ta Musanta Biyan Kuɗin Fansa Domin Kuɓutar da Mutane 360

Da yake yi wa manema labarai jawabi a ranar Juma’a, Bello ya tabbatar da cewa tuni suka fara tattaunawa da shugabannin ADC domin fara shirin ceto kasar nan daga hannun jam’iyya mai mulki.

Ya ce, “Eh, mun fara tattaunawa. Ba ma tsoron hadewa gaba daya. Mu duba tarihin zabe. PRP ita ce jam’iyyar siyasa mafi tsufa a yau. Mun kafa gwamnati a Kaduna a shekarar 1979, saboda kawancen siyasa da jam’iyyun UPN, NPP, da PNP a jihar.

“Idan sauran jam’iyyu suna son shiga cikinmu, to muna maraba da su. Kofofinmu a bude suke ga kowa da kowa hatta daidaikun mutane, ba jam’iyyun siyasa kadai ba. Amma idan sun gwammace su shiga jam’iyyar da ba ta son jama’a da maganar kudi kawai, su koma PDP da APC. Abin da suka tsaya a kai kenan.

“Don haka muna cewa mun gaji kuma muna son wani sabon sauyi. Idan kuma hakan ya bukaci ni ko shugaban jam’iyyar ADC ya sauka daga mukaminsa, to haka ya kasance. Wannan kasa ta fi mu muhimmanci. Kundin tsarin mulkin jam’iyyar PRP yana wakiltar ka’ida da akidar da muke tsayawa a kai.”

Nwosu ya kuma ce bukatar a hada kai ta kara samun karbuwa sakamakon gano cewa suna da akida daya.

Shugaban jam’iyyar ADC ya bayyana cewa, a halin da ake ciki wahalhalun da ake fama da su a kasar nan bai kamata a ce jama’a sun gaji ba, kuma suna bukatar sabon sauyi.

“Hadin kai da hadin gwiwa wanda a karshe zai haifar da yuwuwar hadaka yana gudana tsakanin PRP da ADC. Me ya sa muke yin haka? gina akidar siyasa da fayyace hangen inda muka dosa.

“Jam’iyyunmu ne suka fara wannan magana ta kawance, ba wai ta mutanen da ke neman mukami ba ne. Wadannan shugabannin jam’iyyun siyasa ne wadanda suke jin cewa ya kamata a samu sauyi a kasar nan kuma suna son ci gaba. A karshe, idan mutanen da ke neman mukami sun shigo dole ne su bi wasu ka’idojin da ya kamata su bi. Damuwarmu game da dimokuradiyya a fili take,” ya kara da cewa.

PRP
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
PRP
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ilimi Ne Babban Makamin Daƙile Ta’addanci — Ministan Tsaro
  • Sulaiman
    Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu
  • Sulaiman
    Gwamnatin Borno Ta Musanta Biyan Kuɗin Fansa Domin Kuɓutar da Mutane 360

MASU ALAKA

Sojoji
Labarai

Ilimi Ne Babban Makamin Daƙile Ta’addanci — Ministan Tsaro

June 8, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno
Labarai

Gwamnatin Borno Ta Musanta Biyan Kuɗin Fansa Domin Kuɓutar da Mutane 360

June 8, 2026
Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji

June 8, 2026
Next Post
Ya Kamata Amurka Ta Janye Cuba Daga Jerin Kasashe Masu Goyon Bayan Ta’addanci

Ya Kamata Amurka Ta Janye Cuba Daga Jerin Kasashe Masu Goyon Bayan Ta’addanci

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Ilimi Ne Babban Makamin Daƙile Ta’addanci — Ministan Tsaro

June 8, 2026
Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

June 8, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Gwamnatin Borno Ta Musanta Biyan Kuɗin Fansa Domin Kuɓutar da Mutane 360

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

June 8, 2026
Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji

June 8, 2026
Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

June 8, 2026
Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

June 8, 2026
Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

June 8, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.