‘Yan sa-kai biyu sun rasa rayukansu yayin da wani bam da ake zargin mayaÆ™an Boko Haram ne suka dasa a Æ™aramar hukumar Gujba ta Jihar Yobe.
Masani kan harkokin tsaro, Zagazola Makama, ya bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar Juma’a, 27 ga watan Satumba, a kan hanyar Damaturu–Buni Yadi, kusa da ƙauyen Madiya.
- Kasashen Sin Da Afrika Za Su Hada Kai A Bangaren Intanet
- Kotu Ta Dakatar Da PENGASSAN, NNPCL Kan Katse Wa Matatar ÆŠangote ÆŠanyen Mai Da Iskar Gas
Bam ɗin ya tashi da misalin ƙarfe 2:30 na rana, inda ya kashe mutanen nan take.
An gano waÉ—anda suka mutu; Kinnafi Modu mai shekara 35 da Mamman Kasaisa mai shekara 27.
Wasu ‘yan sa-kai biyu kuma sun ji munanan raunuka, inda aka garzaya da su Asibitin Gwamnati na Damaturu.
Jami’an ’yansanda da na leƙen asiri sun kai ziyara wajen, sun taimaka wajen kwashe gawarwakin waɗanda suka rasu.
An ƙara tsaurara tsaro a kan hanyar don hana ƙara kai wasu hare-hare.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp