A ranar Asabar din da ta gabata ne wasu bama-bamai suka kashe mutane 9 a wata tashar mota da ke kauyen Mairari a karamar hukumar Guzamala a jihar Borno.
Kakakin majalisar dokokin jihar Borno Rt. Hon. Abdulkarim Lawan wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Lahadi, ya bayyana matukar kaduwarsa kan yadda ‘yan ta’addar Boko Haram suka dasa Bam a tashar motocin.
- Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu
- Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane
Lamarin wanda ya faru a ranar Asabar da misalin karfe 11 na safe, ya kuma yi sanadin jikkatar da dama daga cikin mutanen kauyen wadanda daga baya aka kwashe su zuwa Monguno da Maiduguri domin kula da lafiyarsu.
Lawan ya kuma jajantawa iyalan wadanda suka mutu da kuma wadanda suka samu raunuka daban-daban sakamakon fashewar.
Ya kuma yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasu ya kuma ba su Aljanatul Firdaus.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp