• English
  • Business News
Sunday, June 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Banda Akwai Doka Da Mun Shiga Gidan Gwamnatin Bauchi Mun Kwato Mulkinmu —Adamu

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Siyasa
0
Banda Akwai Doka Da Mun Shiga Gidan Gwamnatin Bauchi Mun Kwato Mulkinmu —Adamu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya ce, biyaya ga doka da oda ne kawai zai sanya ba za su shiga har cikin gidan gwamnatin jihar Bauchi su kwato mulkinsu da ya suka ya bari ba.

Adamu ya ce, tun asali jihar Bauchi da al’umarta masoya jam’iyyar APC ne, don haka ya nuna kwarin guiwarsa na cewa za su yi wa PDP tumbur a zaben 2023 da ke tafe.

  • “Ba Zamu Raba Wa Mata Da Matasa Akuyoyi Da Sunan Tallafin Sana’a Ba A Bauchi” —Sadique
  • Ina Jin Takaici Da Damuwa Kan Yadda Ake Fita Daga Jam’iyyarmu Ta APC —Abdullahi Adamu

Abdullahi Adamu wanda ya bayyana hakan a jawabin da ya gabatar ranar Alhamis lokacin bikin kaddamar da yakin neman zaben gwamna na jam’iyyar APC tare da mika tutar jam’iyyar ga Air Marshal Sadique Baba Abubakar.

An gudanar da taron a filin wasa na jihar Bauchi, taron kuma ya samu halartar dumbin jama’a daga ciki da wajen jihar.

Adamu ya ce, “Da so samu ne ni Abdullahi Adamu da zan ce ku shiga ku kwato gwamnati da karfin tsiya, to amma saboda sanin doka zamu bi doka, zamu bi ka’ida, kuma in Allah ya so ya yarda, gwamnatin nan ta jihar Bauchi zata tabbata a hannun Air Marshal Sadique Baba Abubakar,”

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6

Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane

“A jihar Bauchi mun yi barin mulki, mata za su fi mu sanin bari, to mun yi barin mulki. Gwamnatin Bauchi, Gwamnatin APC ce, ko ba haka ba ne? In kuwa haka ne ya aka yi yau Mulki ba ya hannunmu? Ko me ma ya faru, cikin ikon Allah lokacin sake sabon zubi ya yi, za a yi sabon zabe.

“Ranar 25 ga watan Afrilu za a yi zaben shugaban kasa wanda dukkaninmu hankalinmu ya taru mu zabi Bola Ahmed Tinubu a matsayin shugaban Nijeriya. In Muna son a yi tafiya mai riba ya kamata idan muna da shugaban kasa dan APC to a samu gwamnan Jiha dan APC.

“Mu yi wa kanmu adalci mu samu dan APC a gidan gwamnati a ofishin gwamnan Jihar Bauchi, wannan bawan Allah kuwa shi ne, Air Marshal Sadique Baba Abubakar.” Cewar Shugaban Jam’iyyar APC, Abdullahi Adamu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NDLEA Ta Kwace Miyagun Kwayoyi Na Biliyan 450 A Wata 22 – Buba Marwa

Next Post

GORON JUMA’A

Related

Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6

2 days ago
Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane
Manyan Labarai

Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane

3 days ago
A Bai Wa Kudu Tikitin Takara A 2027 Ko PDP Ta Ruguje – Wani Jigo A PDP
Siyasa

A Bai Wa Kudu Tikitin Takara A 2027 Ko PDP Ta Ruguje – Wani Jigo A PDP

4 days ago
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

2 weeks ago
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike
Siyasa

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

2 weeks ago
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya
Siyasa

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

2 weeks ago
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka

NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka

June 15, 2025
Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda

Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda

June 15, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa

NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa

June 15, 2025
Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

June 15, 2025
UEFA

‘Yan Wasa Biyar Da Suka Taka Rawar Gani A Kofin Zakarun Turai

June 15, 2025
An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 

An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 

June 15, 2025
Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran

Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran

June 14, 2025
Za A Watsa Shirin “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” A Kafofin Watsa Shirye-shiryen Kasashen Tsakiyar Asiya Biyar

Za A Watsa Shirin “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” A Kafofin Watsa Shirye-shiryen Kasashen Tsakiyar Asiya Biyar

June 14, 2025
Muhammad Salah: Gwarzon Afirka A Firimiyar Ingila

Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila

June 14, 2025
Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba

Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba

June 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.