Dakarun bangarori biyu na Sudan dake dauki ba dadi, sun zargi juna da kaddamar da hari kan jerin gwanon motocin dake samar da agajin jin kai na Majalisar Dinkin Duniya. Motocin dai sun fuskanci barin wuta ne a daren ranar Litinin a Al-Koma na yankin Darfur ta arewa, lamarin da ya sabbaba rasuwar jami’an ayyukan jin kai biyar, tare da jikkatar wasu da dama.
Wata sanarwar hadin gwiwa da shirin samar da abinci na Majalisar Dinkin Duniya ko WFP, da asusun UNICEF suka fitar a jiya Talata, ta ce motocin ciki har da manya na dakon kayayyaki 15, suna kan hanyarsu ta zuwa birnin El Fasher mai fama da fari, inda za su kai kayayyakin abinci masu gina jiki lokacin da lamarin ya auku. WFP da UNICEF sun yi Allah wadai da aukuwar wannan lamari, suna musu gargadin cewa hari kan tawagar ma’aikatar jin kai ya sabawa dokokin kasa da kasa.
Game da aukuwar wannan lamari, ma’aikatar harkokin wajen Sudan ta zargi rundunar RSF da kaddamar da harin, ta amfani da jirage marasa matuka, tana mai cewa harin ya tarwatsa manyan motocin dakon kaya da dama, da kone wani jirgin aikin ceto, tare da hallaka wasu direbobi, da jami’an tsaro da fararen hula da dama, baya ga wasu da yawa da suka jikkata.
A wata sanarwar ta daban kuma, hukumar samar da agaji da ayyukan jin kai ta Sudan ko SARHO a takaice wadda ke da alaka da rundunar RSF, ta musanta zargin cewa dakarun RSF ne suka kaddamar da harin, tana mai cewa dakarun gwamnati na SAF ne suka kaddamar da harin ta sama kan jerin gwanon motocin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp