Rundunar ‘yansandan Jihar Kebbi ta samu nasarar gano manyan igiyoyi da babura da wasu da ake zargin ‘yan fashi ne suka bari a wajen wani sintiri a gundumar Ribah da ke karamar Hukumar Danko/Wasagu.
- Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan, CSP Nafiu Abubakar, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata, ya bayyana cewa wadanda ake zargin sun gudu ne bayan sun ga wata tawagar ‘yan sintiri ta hadin gwiwa na jami’an ‘yansanda da ’yan banga a kan hanyar Saki/Unashi da misalin karfe 6:30 na safiyar ranar Litinin “Sun jefar da babura da igiyoyin da aka lalata yayin da suka gudu don gudun kada a kama su,” in ji sanarwar.
Rundunar ‘yan sandan ta samu nasarar cafke kayayyakin da aka kwato, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike domin ganowa tare da kamo wadanda suka aikata laifin.
- Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi
- Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya
Kwamishinan ‘yansandan, Bello Sani, ya yaba wa tawagar ‘yan sintiri bisa gaggawa da suka yi.
Sani ya yi alkawarin cewa rundunar za ta ci gaba da kare muhimman ababen more rayuwa da kuma tabbatar da tsaron lafiyar jama’a.
Ya kuma bukaci mazauna yankin da su kasance cikin shiri kuma su kai rahoto ga ofishin ‘yansanda mafi kusa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp