• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barazanar Da Noman Shinkafa Ke Fuskanta A Arewa

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Barazanar Da Noman Shinkafa Ke Fuskanta A Arewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kokarin samar da wadatacciyar Shinkafar da ake nomawa a Nijeriya na ci gaba da fuskanatar barazana, sakamakon shigo da ita da ake yi daga kasashen ketare.

Har ila yau, tsadar kayan noman Shinkafar da rashin samun cikakken goyon bayan hukumomi da manoman ke fusktanta, na kara zama barazana a wannan fanni.
Wani bincike da Jaridar LEADERSHIP ta gudanar ya nuna irin jajircewa da kuma kokarin da Manoman Shinkafa ke ci gaba da yi domin ganin ta wadata a fadin wannan kasa baki-daya.

  • Bankin Duniya Zai Dawo Da Kadadar Noma Sama Da Miliyan Daya A Arewa

Hakazalika, a bangaren Masana’atun da ake sarrafa Shinkafar da ake nomawa a yankunan Arewa, su ma na ci gaba da kai gauro da mari wajen sarrafa ta da kuma tsaftace ta kamar wadda ake kawowa daga waje.
Wasu daga cikin Masana’antun da ke sarrafa Shinkafar a yankunan sun durkushe, sakamakon karancin samun samfarerar da suke sarrafa, wanda hakan ya jawo rashin ayyukan yi ga masu yin aikin Masana’antun.
Misali, akwai Masana’antar da ake sarrafa Shinkafa ta Jihar Kwara, wadda a halin yanzu ayyukanta ba sa tafiya kamar yadda ya kamata, hakan ya kuma yi sanadiyyar rasa ayyukan da dama na ma’aikatan wannan Masana’anta.

Kazalika, yawan Shinkafar ta gida da ake nomawa a Jihar ta Kwara, ya ragu da kaso mai yawa sakamakon kalubale da suke fuskanta da dama.

Wakazalika, Jaridar ta LEADERSHIP ta ruwaito cewa, Masana’antar da ake sarrafa Shinkafa a garin Ilori a Jihar Kwara da wadda take a garin Offa na Kudancin Jihar, ba su iya samar da yawan Shinkafar da ake bukata ba, sakamakon rashin noma ta da ba a yi ba da dama a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

Mukaddashin Shugaban riko na Kungiyar Manoman Shinkafa na kasa reshen Jihar Kwara (RIFAN), Mal. Muhammed Salihu, ya tabbatar da koma bayan da ake samu na noman Shinkafa a fadin jihar.

Malam Muhammed, ya dora alhakin samun raguwar noman ne kan yadda Gwamnatin Tarayya ta dakatar da shirin aikin noma na (Anchor-Borrowers) da kuma rashin kayan aiki na zamani da ya hada da kamar motar taraktar noma, takin zamani da kuma afkuwar iftila’in ambailyar ruwan sama da aka samu.

Haka zalika, ya sake bayar da misali da alkaluma na tan din Shinkafar da aka noma a jihar, inda ya bayyana cewa, a shekarar 2020 an noma tan 60,000, a shekarar 2021 an noma tan 59,000, inda kuma a shekarar 2022 aka noma tan 25,000.

“A ka’ida kamata ya yi a cikin shekara guda su noma Shinkafa a jihar tasu sau uku, amma sai ga shi sun buge da nomawa sau daya a shekara”, in ji shi.

Har wa yau Mukaddashin Shugaban ya kara da cewa, “Muna fuskantar matsalar ambaliyar ruwa, wanda ke lalata Shinkafar da muka shuka da damuna, akwai kuma matsalar rashin kayan aiki da takin zamani da kuma taraktar yin noma.”
Sannan a cewar tasa, an dakatar da shirin aikin noma na (Anchor-borrowers) tun a shekarar 2021, inda daukacin wadannan matsaloli suka taka rawa wajen koma bayan noman wannan Shinkafa a Jihar ta Kwara.
Shugaban ya kuma yi kira ga Gwamnatin Jihar, ta samar wa da Manoman Shinkafar wadataccen takin zamani da sauran kayan aiki, domin ci gaba da samar da wadatar Shinkafar a jihar.

Bugu da kari a wani rahoto da Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito, farashin Buhun Shinkafar Gida a garin Ilorin, ya kai Naira 41,000 sabanin yadda ake sayarwa a baya kan Naira 27,000.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Dokokin Afirka Ta Kudu Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fitar Da Avocado Da Kasar Sin

Next Post

Mutane 12 Sun Mutu, 80 Sun Jikkata A Bikin Bude Wasanni A Madagascar

Related

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje
Noma Da Kiwo

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

1 day ago
Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir
Noma Da Kiwo

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

3 days ago
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

1 week ago
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

1 week ago
Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

2 weeks ago
Next Post
Mutane 12 Sun Mutu, 80 Sun Jikkata A Bikin Bude Wasanni A Madagascar

Mutane 12 Sun Mutu, 80 Sun Jikkata A Bikin Bude Wasanni A Madagascar

LABARAI MASU NASABA

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.