• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barazanar Da Noman Shinkafa Ke Fuskanta A Arewa

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Barazanar Da Noman Shinkafa Ke Fuskanta A Arewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kokarin samar da wadatacciyar Shinkafar da ake nomawa a Nijeriya na ci gaba da fuskanatar barazana, sakamakon shigo da ita da ake yi daga kasashen ketare.

Har ila yau, tsadar kayan noman Shinkafar da rashin samun cikakken goyon bayan hukumomi da manoman ke fusktanta, na kara zama barazana a wannan fanni.
Wani bincike da Jaridar LEADERSHIP ta gudanar ya nuna irin jajircewa da kuma kokarin da Manoman Shinkafa ke ci gaba da yi domin ganin ta wadata a fadin wannan kasa baki-daya.

  • Bankin Duniya Zai Dawo Da Kadadar Noma Sama Da Miliyan Daya A Arewa

Hakazalika, a bangaren Masana’atun da ake sarrafa Shinkafar da ake nomawa a yankunan Arewa, su ma na ci gaba da kai gauro da mari wajen sarrafa ta da kuma tsaftace ta kamar wadda ake kawowa daga waje.
Wasu daga cikin Masana’antun da ke sarrafa Shinkafar a yankunan sun durkushe, sakamakon karancin samun samfarerar da suke sarrafa, wanda hakan ya jawo rashin ayyukan yi ga masu yin aikin Masana’antun.
Misali, akwai Masana’antar da ake sarrafa Shinkafa ta Jihar Kwara, wadda a halin yanzu ayyukanta ba sa tafiya kamar yadda ya kamata, hakan ya kuma yi sanadiyyar rasa ayyukan da dama na ma’aikatan wannan Masana’anta.

Kazalika, yawan Shinkafar ta gida da ake nomawa a Jihar ta Kwara, ya ragu da kaso mai yawa sakamakon kalubale da suke fuskanta da dama.

Wakazalika, Jaridar ta LEADERSHIP ta ruwaito cewa, Masana’antar da ake sarrafa Shinkafa a garin Ilori a Jihar Kwara da wadda take a garin Offa na Kudancin Jihar, ba su iya samar da yawan Shinkafar da ake bukata ba, sakamakon rashin noma ta da ba a yi ba da dama a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Mukaddashin Shugaban riko na Kungiyar Manoman Shinkafa na kasa reshen Jihar Kwara (RIFAN), Mal. Muhammed Salihu, ya tabbatar da koma bayan da ake samu na noman Shinkafa a fadin jihar.

Malam Muhammed, ya dora alhakin samun raguwar noman ne kan yadda Gwamnatin Tarayya ta dakatar da shirin aikin noma na (Anchor-Borrowers) da kuma rashin kayan aiki na zamani da ya hada da kamar motar taraktar noma, takin zamani da kuma afkuwar iftila’in ambailyar ruwan sama da aka samu.

Haka zalika, ya sake bayar da misali da alkaluma na tan din Shinkafar da aka noma a jihar, inda ya bayyana cewa, a shekarar 2020 an noma tan 60,000, a shekarar 2021 an noma tan 59,000, inda kuma a shekarar 2022 aka noma tan 25,000.

“A ka’ida kamata ya yi a cikin shekara guda su noma Shinkafa a jihar tasu sau uku, amma sai ga shi sun buge da nomawa sau daya a shekara”, in ji shi.

Har wa yau Mukaddashin Shugaban ya kara da cewa, “Muna fuskantar matsalar ambaliyar ruwa, wanda ke lalata Shinkafar da muka shuka da damuna, akwai kuma matsalar rashin kayan aiki da takin zamani da kuma taraktar yin noma.”
Sannan a cewar tasa, an dakatar da shirin aikin noma na (Anchor-borrowers) tun a shekarar 2021, inda daukacin wadannan matsaloli suka taka rawa wajen koma bayan noman wannan Shinkafa a Jihar ta Kwara.
Shugaban ya kuma yi kira ga Gwamnatin Jihar, ta samar wa da Manoman Shinkafar wadataccen takin zamani da sauran kayan aiki, domin ci gaba da samar da wadatar Shinkafar a jihar.

Bugu da kari a wani rahoto da Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito, farashin Buhun Shinkafar Gida a garin Ilorin, ya kai Naira 41,000 sabanin yadda ake sayarwa a baya kan Naira 27,000.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Dokokin Afirka Ta Kudu Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fitar Da Avocado Da Kasar Sin

Next Post

Mutane 12 Sun Mutu, 80 Sun Jikkata A Bikin Bude Wasanni A Madagascar

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

1 week ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

1 week ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

3 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

3 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

1 month ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

1 month ago
Next Post
Mutane 12 Sun Mutu, 80 Sun Jikkata A Bikin Bude Wasanni A Madagascar

Mutane 12 Sun Mutu, 80 Sun Jikkata A Bikin Bude Wasanni A Madagascar

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.