• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barazanar Da Noman Shinkafa Ke Fuskanta A Arewa

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Barazanar Da Noman Shinkafa Ke Fuskanta A Arewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kokarin samar da wadatacciyar Shinkafar da ake nomawa a Nijeriya na ci gaba da fuskanatar barazana, sakamakon shigo da ita da ake yi daga kasashen ketare.

Har ila yau, tsadar kayan noman Shinkafar da rashin samun cikakken goyon bayan hukumomi da manoman ke fusktanta, na kara zama barazana a wannan fanni.
Wani bincike da Jaridar LEADERSHIP ta gudanar ya nuna irin jajircewa da kuma kokarin da Manoman Shinkafa ke ci gaba da yi domin ganin ta wadata a fadin wannan kasa baki-daya.

  • Bankin Duniya Zai Dawo Da Kadadar Noma Sama Da Miliyan Daya A Arewa

Hakazalika, a bangaren Masana’atun da ake sarrafa Shinkafar da ake nomawa a yankunan Arewa, su ma na ci gaba da kai gauro da mari wajen sarrafa ta da kuma tsaftace ta kamar wadda ake kawowa daga waje.
Wasu daga cikin Masana’antun da ke sarrafa Shinkafar a yankunan sun durkushe, sakamakon karancin samun samfarerar da suke sarrafa, wanda hakan ya jawo rashin ayyukan yi ga masu yin aikin Masana’antun.
Misali, akwai Masana’antar da ake sarrafa Shinkafa ta Jihar Kwara, wadda a halin yanzu ayyukanta ba sa tafiya kamar yadda ya kamata, hakan ya kuma yi sanadiyyar rasa ayyukan da dama na ma’aikatan wannan Masana’anta.

Kazalika, yawan Shinkafar ta gida da ake nomawa a Jihar ta Kwara, ya ragu da kaso mai yawa sakamakon kalubale da suke fuskanta da dama.

Wakazalika, Jaridar ta LEADERSHIP ta ruwaito cewa, Masana’antar da ake sarrafa Shinkafa a garin Ilori a Jihar Kwara da wadda take a garin Offa na Kudancin Jihar, ba su iya samar da yawan Shinkafar da ake bukata ba, sakamakon rashin noma ta da ba a yi ba da dama a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

Mukaddashin Shugaban riko na Kungiyar Manoman Shinkafa na kasa reshen Jihar Kwara (RIFAN), Mal. Muhammed Salihu, ya tabbatar da koma bayan da ake samu na noman Shinkafa a fadin jihar.

Malam Muhammed, ya dora alhakin samun raguwar noman ne kan yadda Gwamnatin Tarayya ta dakatar da shirin aikin noma na (Anchor-Borrowers) da kuma rashin kayan aiki na zamani da ya hada da kamar motar taraktar noma, takin zamani da kuma afkuwar iftila’in ambailyar ruwan sama da aka samu.

Haka zalika, ya sake bayar da misali da alkaluma na tan din Shinkafar da aka noma a jihar, inda ya bayyana cewa, a shekarar 2020 an noma tan 60,000, a shekarar 2021 an noma tan 59,000, inda kuma a shekarar 2022 aka noma tan 25,000.

“A ka’ida kamata ya yi a cikin shekara guda su noma Shinkafa a jihar tasu sau uku, amma sai ga shi sun buge da nomawa sau daya a shekara”, in ji shi.

Har wa yau Mukaddashin Shugaban ya kara da cewa, “Muna fuskantar matsalar ambaliyar ruwa, wanda ke lalata Shinkafar da muka shuka da damuna, akwai kuma matsalar rashin kayan aiki da takin zamani da kuma taraktar yin noma.”
Sannan a cewar tasa, an dakatar da shirin aikin noma na (Anchor-borrowers) tun a shekarar 2021, inda daukacin wadannan matsaloli suka taka rawa wajen koma bayan noman wannan Shinkafa a Jihar ta Kwara.
Shugaban ya kuma yi kira ga Gwamnatin Jihar, ta samar wa da Manoman Shinkafar wadataccen takin zamani da sauran kayan aiki, domin ci gaba da samar da wadatar Shinkafar a jihar.

Bugu da kari a wani rahoto da Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito, farashin Buhun Shinkafar Gida a garin Ilorin, ya kai Naira 41,000 sabanin yadda ake sayarwa a baya kan Naira 27,000.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Dokokin Afirka Ta Kudu Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fitar Da Avocado Da Kasar Sin

Next Post

Mutane 12 Sun Mutu, 80 Sun Jikkata A Bikin Bude Wasanni A Madagascar

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

4 days ago
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

5 days ago
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet
Noma Da Kiwo

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

5 days ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

5 days ago
Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

2 weeks ago
Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja
Noma Da Kiwo

Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja

2 weeks ago
Next Post
Mutane 12 Sun Mutu, 80 Sun Jikkata A Bikin Bude Wasanni A Madagascar

Mutane 12 Sun Mutu, 80 Sun Jikkata A Bikin Bude Wasanni A Madagascar

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.