ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

by Abubakar Abba
8 months ago
Tinubu

Gwamnan Jihar Ekiti, Mista Biodun Oyebanji, ya yaba wa shirin aikin noma na Shugaban Kasa Bola Tinubu (Renewed Hope), wanda ya ce; shirin zai kara wa mutane da dama kwarin gwiwar rungumar aikin manoma.

Kazalika, Oyebanji ya yaba da shirin, musamman duba da cewa; ana gudanar da shi ne ta hanyar yin amfani da fasahar zamani ta noma, wanda ya yi nuni da cewa; hakan zai jawo ra’ayin matasan jihar su rungumi aikin noma, inda hakan zai ba su damar bayar da tasu gudunmwar, wajen samar da wadataccen abinci a jihar ta Ekiti.

  • Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji
  • Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Ya bayyana hakan ne, a yayin kaddamar da farfado da wani katafaren gidan gona da ke yankin Eporo Ekiti, a Karamar Hukumar Emure da ke jihar.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, an kaddamar da gidan gonar ne daga cikin shirye-shiyen gudanar da bikin cikar gwamnan shekara uku a wa’adin shugabancinsa.

Kazalika, gwamnan ya kuma kaddamar farfado da wasu gidajen gona uku da ke yankunan Iyemero da kuma Ikere Ekiti, bisa nufin kara samar da wadataccen abinci a jihar, musamman domin rage farashin kayan abinci a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Gidajen gidan gonar uku, na daga cikin ayyukan shirin aikin gona da aka farfado da su, domin bai wa matasan da ke da sha’awar shiga aikin noma tare da kuma yin kiwon Kifi.

Gwamnan, wanda mataimakiyarsa, Madam Monisade Afuye ta wakilce shi a wajen taron ya sanar da cewa, baya ga sake farfado da gidajen gonar, wadanda firimiyan tsohuwar gwamnatin yamma, Cif Obafemi Awolowo ya samar da su, an kuma samar da wasu guda 13, domin bai wa matasan da ke yankin kwarin guiwar shiga aikin noma.

Kazalika, gwamnan ya bayyana cewa; an kuma samar da kayan aiki na zamani, wadanda za su bai wa matasan damar yin noma har zuwa karshen shekara, musamman domin inganta rayuwarsu da samar wa da kawunansu kudaden shiga da kuma yadda za su taimaka wa iyayaensu.

“Wadannan gidajen gona da muka kaddamar da su yau a yankunan Eporo, Emure da Iyemero, an sake farfado da su ne, domin a bai wa manoma kwarin gwiwar yadda za su rungumi aikin noma, domin su zama masu dogaro da kansu,“ in ji gwamnan.

“Kimanin matasa 5,000 zuwa yanzu aka dauka a karkashin wannnan shiri, musamman duba da cewa; matasan sun nuna cewa; a shirye suke su shiga aikin noma,” a cewar tasa.

“Muna kuma sane da marasa kishin da ke yunkurin yi wa wannan shiri zagon kasa, domin su ga cewa, aikin bai samu cin nasara ba, amma ina ba ku tabbacin cewa; na ci gaba da yin aiki da hukumomin tsaro, domin a bai wa wadannan gonaki kariyar da ta kamata daga wadannan marasa kishin, musamman domin wadanda za su amfana, su yi aiki a cikin gonakin, ba tare da fuskantar wata barazana ko yin garkuwa da su ba,” in ji Oyebanji.

Shi ma a nasa jawabin a wajen taron, kwamishinan ma’aikatar aikin gona da samar da wadataccen abinci na jihar, Mista Ebenezer Boluwade ya bayyana cewa; kimanin manoma 200 ne za su iya yin noma a gidan gonar ta Eporo Ekiti, wadda kuma aka samar mata da kayan aiki na zamani da suka hada da na’urorin samar da hasken wuta ta sola da sauran makamantansu.

Tinubu
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.