ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

by Abubakar Abba
7 months ago
Tinubu

Gwamnan Jihar Ekiti, Mista Biodun Oyebanji, ya yaba wa shirin aikin noma na Shugaban Kasa Bola Tinubu (Renewed Hope), wanda ya ce; shirin zai kara wa mutane da dama kwarin gwiwar rungumar aikin manoma.

Kazalika, Oyebanji ya yaba da shirin, musamman duba da cewa; ana gudanar da shi ne ta hanyar yin amfani da fasahar zamani ta noma, wanda ya yi nuni da cewa; hakan zai jawo ra’ayin matasan jihar su rungumi aikin noma, inda hakan zai ba su damar bayar da tasu gudunmwar, wajen samar da wadataccen abinci a jihar ta Ekiti.

  • Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji
  • Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Ya bayyana hakan ne, a yayin kaddamar da farfado da wani katafaren gidan gona da ke yankin Eporo Ekiti, a Karamar Hukumar Emure da ke jihar.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, an kaddamar da gidan gonar ne daga cikin shirye-shiyen gudanar da bikin cikar gwamnan shekara uku a wa’adin shugabancinsa.

Kazalika, gwamnan ya kuma kaddamar farfado da wasu gidajen gona uku da ke yankunan Iyemero da kuma Ikere Ekiti, bisa nufin kara samar da wadataccen abinci a jihar, musamman domin rage farashin kayan abinci a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Gidajen gidan gonar uku, na daga cikin ayyukan shirin aikin gona da aka farfado da su, domin bai wa matasan da ke da sha’awar shiga aikin noma tare da kuma yin kiwon Kifi.

Gwamnan, wanda mataimakiyarsa, Madam Monisade Afuye ta wakilce shi a wajen taron ya sanar da cewa, baya ga sake farfado da gidajen gonar, wadanda firimiyan tsohuwar gwamnatin yamma, Cif Obafemi Awolowo ya samar da su, an kuma samar da wasu guda 13, domin bai wa matasan da ke yankin kwarin guiwar shiga aikin noma.

Kazalika, gwamnan ya bayyana cewa; an kuma samar da kayan aiki na zamani, wadanda za su bai wa matasan damar yin noma har zuwa karshen shekara, musamman domin inganta rayuwarsu da samar wa da kawunansu kudaden shiga da kuma yadda za su taimaka wa iyayaensu.

“Wadannan gidajen gona da muka kaddamar da su yau a yankunan Eporo, Emure da Iyemero, an sake farfado da su ne, domin a bai wa manoma kwarin gwiwar yadda za su rungumi aikin noma, domin su zama masu dogaro da kansu,“ in ji gwamnan.

“Kimanin matasa 5,000 zuwa yanzu aka dauka a karkashin wannnan shiri, musamman duba da cewa; matasan sun nuna cewa; a shirye suke su shiga aikin noma,” a cewar tasa.

“Muna kuma sane da marasa kishin da ke yunkurin yi wa wannan shiri zagon kasa, domin su ga cewa, aikin bai samu cin nasara ba, amma ina ba ku tabbacin cewa; na ci gaba da yin aiki da hukumomin tsaro, domin a bai wa wadannan gonaki kariyar da ta kamata daga wadannan marasa kishin, musamman domin wadanda za su amfana, su yi aiki a cikin gonakin, ba tare da fuskantar wata barazana ko yin garkuwa da su ba,” in ji Oyebanji.

Shi ma a nasa jawabin a wajen taron, kwamishinan ma’aikatar aikin gona da samar da wadataccen abinci na jihar, Mista Ebenezer Boluwade ya bayyana cewa; kimanin manoma 200 ne za su iya yin noma a gidan gonar ta Eporo Ekiti, wadda kuma aka samar mata da kayan aiki na zamani da suka hada da na’urorin samar da hasken wuta ta sola da sauran makamantansu.

Tinubu
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.