ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

by Abubakar Abba
10 months ago
Tinubu

Gwamnan Jihar Ekiti, Mista Biodun Oyebanji, ya yaba wa shirin aikin noma na Shugaban Kasa Bola Tinubu (Renewed Hope), wanda ya ce; shirin zai kara wa mutane da dama kwarin gwiwar rungumar aikin manoma.

Kazalika, Oyebanji ya yaba da shirin, musamman duba da cewa; ana gudanar da shi ne ta hanyar yin amfani da fasahar zamani ta noma, wanda ya yi nuni da cewa; hakan zai jawo ra’ayin matasan jihar su rungumi aikin noma, inda hakan zai ba su damar bayar da tasu gudunmwar, wajen samar da wadataccen abinci a jihar ta Ekiti.

  • Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji
  • Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Ya bayyana hakan ne, a yayin kaddamar da farfado da wani katafaren gidan gona da ke yankin Eporo Ekiti, a Karamar Hukumar Emure da ke jihar.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, an kaddamar da gidan gonar ne daga cikin shirye-shiyen gudanar da bikin cikar gwamnan shekara uku a wa’adin shugabancinsa.

Kazalika, gwamnan ya kuma kaddamar farfado da wasu gidajen gona uku da ke yankunan Iyemero da kuma Ikere Ekiti, bisa nufin kara samar da wadataccen abinci a jihar, musamman domin rage farashin kayan abinci a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Gidajen gidan gonar uku, na daga cikin ayyukan shirin aikin gona da aka farfado da su, domin bai wa matasan da ke da sha’awar shiga aikin noma tare da kuma yin kiwon Kifi.

Gwamnan, wanda mataimakiyarsa, Madam Monisade Afuye ta wakilce shi a wajen taron ya sanar da cewa, baya ga sake farfado da gidajen gonar, wadanda firimiyan tsohuwar gwamnatin yamma, Cif Obafemi Awolowo ya samar da su, an kuma samar da wasu guda 13, domin bai wa matasan da ke yankin kwarin guiwar shiga aikin noma.

Kazalika, gwamnan ya bayyana cewa; an kuma samar da kayan aiki na zamani, wadanda za su bai wa matasan damar yin noma har zuwa karshen shekara, musamman domin inganta rayuwarsu da samar wa da kawunansu kudaden shiga da kuma yadda za su taimaka wa iyayaensu.

“Wadannan gidajen gona da muka kaddamar da su yau a yankunan Eporo, Emure da Iyemero, an sake farfado da su ne, domin a bai wa manoma kwarin gwiwar yadda za su rungumi aikin noma, domin su zama masu dogaro da kansu,“ in ji gwamnan.

“Kimanin matasa 5,000 zuwa yanzu aka dauka a karkashin wannnan shiri, musamman duba da cewa; matasan sun nuna cewa; a shirye suke su shiga aikin noma,” a cewar tasa.

“Muna kuma sane da marasa kishin da ke yunkurin yi wa wannan shiri zagon kasa, domin su ga cewa, aikin bai samu cin nasara ba, amma ina ba ku tabbacin cewa; na ci gaba da yin aiki da hukumomin tsaro, domin a bai wa wadannan gonaki kariyar da ta kamata daga wadannan marasa kishin, musamman domin wadanda za su amfana, su yi aiki a cikin gonakin, ba tare da fuskantar wata barazana ko yin garkuwa da su ba,” in ji Oyebanji.

Shi ma a nasa jawabin a wajen taron, kwamishinan ma’aikatar aikin gona da samar da wadataccen abinci na jihar, Mista Ebenezer Boluwade ya bayyana cewa; kimanin manoma 200 ne za su iya yin noma a gidan gonar ta Eporo Ekiti, wadda kuma aka samar mata da kayan aiki na zamani da suka hada da na’urorin samar da hasken wuta ta sola da sauran makamantansu.

Tinubu
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.