ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

by Abubakar Abba
8 months ago
Tinubu

Gwamnan Jihar Ekiti, Mista Biodun Oyebanji, ya yaba wa shirin aikin noma na Shugaban Kasa Bola Tinubu (Renewed Hope), wanda ya ce; shirin zai kara wa mutane da dama kwarin gwiwar rungumar aikin manoma.

Kazalika, Oyebanji ya yaba da shirin, musamman duba da cewa; ana gudanar da shi ne ta hanyar yin amfani da fasahar zamani ta noma, wanda ya yi nuni da cewa; hakan zai jawo ra’ayin matasan jihar su rungumi aikin noma, inda hakan zai ba su damar bayar da tasu gudunmwar, wajen samar da wadataccen abinci a jihar ta Ekiti.

  • Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji
  • Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Ya bayyana hakan ne, a yayin kaddamar da farfado da wani katafaren gidan gona da ke yankin Eporo Ekiti, a Karamar Hukumar Emure da ke jihar.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, an kaddamar da gidan gonar ne daga cikin shirye-shiyen gudanar da bikin cikar gwamnan shekara uku a wa’adin shugabancinsa.

Kazalika, gwamnan ya kuma kaddamar farfado da wasu gidajen gona uku da ke yankunan Iyemero da kuma Ikere Ekiti, bisa nufin kara samar da wadataccen abinci a jihar, musamman domin rage farashin kayan abinci a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Gidajen gidan gonar uku, na daga cikin ayyukan shirin aikin gona da aka farfado da su, domin bai wa matasan da ke da sha’awar shiga aikin noma tare da kuma yin kiwon Kifi.

Gwamnan, wanda mataimakiyarsa, Madam Monisade Afuye ta wakilce shi a wajen taron ya sanar da cewa, baya ga sake farfado da gidajen gonar, wadanda firimiyan tsohuwar gwamnatin yamma, Cif Obafemi Awolowo ya samar da su, an kuma samar da wasu guda 13, domin bai wa matasan da ke yankin kwarin guiwar shiga aikin noma.

Kazalika, gwamnan ya bayyana cewa; an kuma samar da kayan aiki na zamani, wadanda za su bai wa matasan damar yin noma har zuwa karshen shekara, musamman domin inganta rayuwarsu da samar wa da kawunansu kudaden shiga da kuma yadda za su taimaka wa iyayaensu.

“Wadannan gidajen gona da muka kaddamar da su yau a yankunan Eporo, Emure da Iyemero, an sake farfado da su ne, domin a bai wa manoma kwarin gwiwar yadda za su rungumi aikin noma, domin su zama masu dogaro da kansu,“ in ji gwamnan.

“Kimanin matasa 5,000 zuwa yanzu aka dauka a karkashin wannnan shiri, musamman duba da cewa; matasan sun nuna cewa; a shirye suke su shiga aikin noma,” a cewar tasa.

“Muna kuma sane da marasa kishin da ke yunkurin yi wa wannan shiri zagon kasa, domin su ga cewa, aikin bai samu cin nasara ba, amma ina ba ku tabbacin cewa; na ci gaba da yin aiki da hukumomin tsaro, domin a bai wa wadannan gonaki kariyar da ta kamata daga wadannan marasa kishin, musamman domin wadanda za su amfana, su yi aiki a cikin gonakin, ba tare da fuskantar wata barazana ko yin garkuwa da su ba,” in ji Oyebanji.

Shi ma a nasa jawabin a wajen taron, kwamishinan ma’aikatar aikin gona da samar da wadataccen abinci na jihar, Mista Ebenezer Boluwade ya bayyana cewa; kimanin manoma 200 ne za su iya yin noma a gidan gonar ta Eporo Ekiti, wadda kuma aka samar mata da kayan aiki na zamani da suka hada da na’urorin samar da hasken wuta ta sola da sauran makamantansu.

Tinubu
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.