• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barista Aysha Ahmad: Gwarzuwar Tabbatar Da Adalci Da Dogaro Da Kai

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
in Adon Gari
0
Barista Aysha Ahmad: Gwarzuwar Tabbatar Da Adalci Da Dogaro Da Kai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Barista Aysha Ahmad, kwararriyar lauya ce kuma mai ba da shawarwari ta fuskar Shari’a da harkokin rayuwa, wacce ta tsaya tsayin daka wajen kawo sauyi da karfafa samar da ayyukan dogaro da kai a garinta na haihuwa Zariya da ke Jihar Kaduna. Haifaffiyar garin Zariya ce, birni mai cike da tarihi da al’adu.

Ta yi karatu a Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, inda ta samu digiri a fannin zama kwararriyar lauya (LLB). Daga nan ta samu nasarar shiga makarantar lauyoyi ta Nijeriya tare da cimma nasarori masu dimbin yawa a shekarar 2005.

  • Jarin Da Sin Ta Zuba A Bangaren Sufuri Ya Karu A Cikin Watanni 11 Na Farkon 2023
  • Amurka Ta Lalata Manufarta Ta Fadin Albarkacin Baki Wajen Watsa Labarai

A kokarinta na fadada neman kwarewa a fannin karatun shari’a, Barr Aysha Ahmad ta wuce zuwa kasar Ingila inda ta samu digirinta na biyu a fannin shari’a a Jami’ar Salford da ke kasar, inda ta karfafa iliminta tare da samun kwarewa a fannonin zamantakewar Duniya.

A daya bangaren kuma, Barr Aysha Ahmad ita ce shugaba kuma mamallakiyar Kamfanin Lauyoyi na Essence Chambers, kamfanin da ya kware wajen tsayawa da wakiltar ‘ya’ya mata da kananan yara Hausa/Fulani a kafatanin Garin Zariya a bangaren shari’a.

Aysha

Labarai Masu Nasaba

Ko Kin San… Dalilin Da Ke Sa Mata Ke Ganin Farin Ruwa Kafin Ko Bayan Al’adarsu?

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Wannan ke kara jaddada sadaukarwarta don warware shinge da tufka da warwara a cikin aikin tabbatar da adalci.

Tasirinta bai tsaya a kotu kadai ba, domin yunkurin da ta yi na kawo sauyi a zamantakewa ya sa ta kafa gidauniyar kula da yara mata ta sarauniya wato (Sarauniya Girls Child Care Foundation).

Aysha
Wannan gidauniya ta zama hanyar jinkai da share hawaye ga masu karamin karfi a fadin birni da karkara a Nijeriya, ta hanyar samar da sabbin tsare-tsaren yaki da fatara gami da samar da Tallafi.

Aysha Ahmad ta sadaukar da kanta ga inganta rayuwar marasa galihu, musamman ‘yan mata, tare da samar da guraben ayyukan dogaro da kai ya sa ta samu matukar karbuwa sosai a tsakanin al’umma.

Aysha
Ta kasance mai yawan halartar tarukan kara wa juna sani da manyan tarukan al’umma wanda wannan ya kara haskaka kwarewarta a duniya.

Bayan dimbin yabo da take samu daga ba’arin mutane, ta zama abin koyi ga mutane da yawa masu burin ganin sun kwaikwayi ayyukanta na tausayin al’umma, har ma aka yi mata lakabi da Jagorar Tabbatar da Adalci da Ayyukan Jin kan Al’umma, wato ‘Icon of Justice & Humanitarian Serbices’, Saboda jajircewarta wajen tsayawa kan gaskiya, daidaito, da ci gaban al’umma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaSinXinjiang
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jarin Da Sin Ta Zuba A Bangaren Sufuri Ya Karu A Cikin Watanni 11 Na Farkon 2023

Next Post

Sin Ta Yanke Shawarar Kakaba Takunkumi Ga Kamfanonin Tsaron Amurka Guda Biyar

Related

tusar gaba
Adon Gari

Ko Kin San… Dalilin Da Ke Sa Mata Ke Ganin Farin Ruwa Kafin Ko Bayan Al’adarsu?

3 weeks ago
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Ado Da Kwalliya

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

2 months ago
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Adon Gari

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

2 months ago
Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure
Adon Gari

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

4 months ago
Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

5 months ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

7 months ago
Next Post
Sin Ta Yanke Shawarar Kakaba Takunkumi Ga Kamfanonin Tsaron Amurka Guda Biyar

Sin Ta Yanke Shawarar Kakaba Takunkumi Ga Kamfanonin Tsaron Amurka Guda Biyar

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.