• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barista Aysha Ahmad: Gwarzuwar Tabbatar Da Adalci Da Dogaro Da Kai

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
in Adon Gari
0
Barista Aysha Ahmad: Gwarzuwar Tabbatar Da Adalci Da Dogaro Da Kai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Barista Aysha Ahmad, kwararriyar lauya ce kuma mai ba da shawarwari ta fuskar Shari’a da harkokin rayuwa, wacce ta tsaya tsayin daka wajen kawo sauyi da karfafa samar da ayyukan dogaro da kai a garinta na haihuwa Zariya da ke Jihar Kaduna. Haifaffiyar garin Zariya ce, birni mai cike da tarihi da al’adu.

Ta yi karatu a Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, inda ta samu digiri a fannin zama kwararriyar lauya (LLB). Daga nan ta samu nasarar shiga makarantar lauyoyi ta Nijeriya tare da cimma nasarori masu dimbin yawa a shekarar 2005.

  • Jarin Da Sin Ta Zuba A Bangaren Sufuri Ya Karu A Cikin Watanni 11 Na Farkon 2023
  • Amurka Ta Lalata Manufarta Ta Fadin Albarkacin Baki Wajen Watsa Labarai

A kokarinta na fadada neman kwarewa a fannin karatun shari’a, Barr Aysha Ahmad ta wuce zuwa kasar Ingila inda ta samu digirinta na biyu a fannin shari’a a Jami’ar Salford da ke kasar, inda ta karfafa iliminta tare da samun kwarewa a fannonin zamantakewar Duniya.

A daya bangaren kuma, Barr Aysha Ahmad ita ce shugaba kuma mamallakiyar Kamfanin Lauyoyi na Essence Chambers, kamfanin da ya kware wajen tsayawa da wakiltar ‘ya’ya mata da kananan yara Hausa/Fulani a kafatanin Garin Zariya a bangaren shari’a.

Aysha

Labarai Masu Nasaba

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Wannan ke kara jaddada sadaukarwarta don warware shinge da tufka da warwara a cikin aikin tabbatar da adalci.

Tasirinta bai tsaya a kotu kadai ba, domin yunkurin da ta yi na kawo sauyi a zamantakewa ya sa ta kafa gidauniyar kula da yara mata ta sarauniya wato (Sarauniya Girls Child Care Foundation).

Aysha
Wannan gidauniya ta zama hanyar jinkai da share hawaye ga masu karamin karfi a fadin birni da karkara a Nijeriya, ta hanyar samar da sabbin tsare-tsaren yaki da fatara gami da samar da Tallafi.

Aysha Ahmad ta sadaukar da kanta ga inganta rayuwar marasa galihu, musamman ‘yan mata, tare da samar da guraben ayyukan dogaro da kai ya sa ta samu matukar karbuwa sosai a tsakanin al’umma.

Aysha
Ta kasance mai yawan halartar tarukan kara wa juna sani da manyan tarukan al’umma wanda wannan ya kara haskaka kwarewarta a duniya.

Bayan dimbin yabo da take samu daga ba’arin mutane, ta zama abin koyi ga mutane da yawa masu burin ganin sun kwaikwayi ayyukanta na tausayin al’umma, har ma aka yi mata lakabi da Jagorar Tabbatar da Adalci da Ayyukan Jin kan Al’umma, wato ‘Icon of Justice & Humanitarian Serbices’, Saboda jajircewarta wajen tsayawa kan gaskiya, daidaito, da ci gaban al’umma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaSinXinjiang
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jarin Da Sin Ta Zuba A Bangaren Sufuri Ya Karu A Cikin Watanni 11 Na Farkon 2023

Next Post

Sin Ta Yanke Shawarar Kakaba Takunkumi Ga Kamfanonin Tsaron Amurka Guda Biyar

Related

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Ado Da Kwalliya

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

3 weeks ago
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Adon Gari

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

4 weeks ago
Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure
Adon Gari

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

3 months ago
Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

4 months ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

7 months ago
Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar
Adon Gari

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

7 months ago
Next Post
Sin Ta Yanke Shawarar Kakaba Takunkumi Ga Kamfanonin Tsaron Amurka Guda Biyar

Sin Ta Yanke Shawarar Kakaba Takunkumi Ga Kamfanonin Tsaron Amurka Guda Biyar

LABARAI MASU NASABA

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.