ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barista Aysha Ahmad: Gwarzuwar Tabbatar Da Adalci Da Dogaro Da Kai

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Aysha

Barista Aysha Ahmad, kwararriyar lauya ce kuma mai ba da shawarwari ta fuskar Shari’a da harkokin rayuwa, wacce ta tsaya tsayin daka wajen kawo sauyi da karfafa samar da ayyukan dogaro da kai a garinta na haihuwa Zariya da ke Jihar Kaduna. Haifaffiyar garin Zariya ce, birni mai cike da tarihi da al’adu.

Ta yi karatu a Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, inda ta samu digiri a fannin zama kwararriyar lauya (LLB). Daga nan ta samu nasarar shiga makarantar lauyoyi ta Nijeriya tare da cimma nasarori masu dimbin yawa a shekarar 2005.

  • Jarin Da Sin Ta Zuba A Bangaren Sufuri Ya Karu A Cikin Watanni 11 Na Farkon 2023
  • Amurka Ta Lalata Manufarta Ta Fadin Albarkacin Baki Wajen Watsa Labarai

A kokarinta na fadada neman kwarewa a fannin karatun shari’a, Barr Aysha Ahmad ta wuce zuwa kasar Ingila inda ta samu digirinta na biyu a fannin shari’a a Jami’ar Salford da ke kasar, inda ta karfafa iliminta tare da samun kwarewa a fannonin zamantakewar Duniya.

ADVERTISEMENT

A daya bangaren kuma, Barr Aysha Ahmad ita ce shugaba kuma mamallakiyar Kamfanin Lauyoyi na Essence Chambers, kamfanin da ya kware wajen tsayawa da wakiltar ‘ya’ya mata da kananan yara Hausa/Fulani a kafatanin Garin Zariya a bangaren shari’a.

Aysha

LABARAI MASU NASABA

Sirrin Mallakar Miji 

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

Wannan ke kara jaddada sadaukarwarta don warware shinge da tufka da warwara a cikin aikin tabbatar da adalci.

Tasirinta bai tsaya a kotu kadai ba, domin yunkurin da ta yi na kawo sauyi a zamantakewa ya sa ta kafa gidauniyar kula da yara mata ta sarauniya wato (Sarauniya Girls Child Care Foundation).

Aysha
Wannan gidauniya ta zama hanyar jinkai da share hawaye ga masu karamin karfi a fadin birni da karkara a Nijeriya, ta hanyar samar da sabbin tsare-tsaren yaki da fatara gami da samar da Tallafi.

Aysha Ahmad ta sadaukar da kanta ga inganta rayuwar marasa galihu, musamman ‘yan mata, tare da samar da guraben ayyukan dogaro da kai ya sa ta samu matukar karbuwa sosai a tsakanin al’umma.

Aysha
Ta kasance mai yawan halartar tarukan kara wa juna sani da manyan tarukan al’umma wanda wannan ya kara haskaka kwarewarta a duniya.

Bayan dimbin yabo da take samu daga ba’arin mutane, ta zama abin koyi ga mutane da yawa masu burin ganin sun kwaikwayi ayyukanta na tausayin al’umma, har ma aka yi mata lakabi da Jagorar Tabbatar da Adalci da Ayyukan Jin kan Al’umma, wato ‘Icon of Justice & Humanitarian Serbices’, Saboda jajircewarta wajen tsayawa kan gaskiya, daidaito, da ci gaban al’umma.

Aysha
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasihar Da Ya Dace Dukkan Iyaye Su Yi Wa ‘Yaƴansu Yayin  Aure?
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa

MASU ALAKA

Sirrin Mallakar Miji 
Adon Gari

Sirrin Mallakar Miji 

January 25, 2026
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

October 12, 2025
Next Post
Sin Ta Yanke Shawarar Kakaba Takunkumi Ga Kamfanonin Tsaron Amurka Guda Biyar

Sin Ta Yanke Shawarar Kakaba Takunkumi Ga Kamfanonin Tsaron Amurka Guda Biyar

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.