ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Basirar Kasar Sin Na Iya Saita Alkiblar Warware Rikicin Palasdinu Da Isra’ila

by CGTN Hausa
2 years ago
Palasdinu

Ministan harkokin wajen Sin Wang Yi, zai tafi birnin New York na Amurka domin jagorantar taron Kwamitin Sulhu na MDD kan rikicin Palasdinu da Isra’ila da za a yi a gobe Laraba.

Kasar Sin ta karbi ragamar shugabancin kwamitin sulhu na MDD a lokaci mai matukar muhimmanci da ido da hankalin duniya ya koma kan rikicin da ake yi tsakanin Isra’ila da kungiyar Hamas ta Palasdinu, wanda ya haifar da asarar rayuka da matsalolin jin kai.

  • Sin Ta Kammala Tsara Aikin Tauraron Dan Adam Mai Nisa Na Farko Domin Samar Da Hidimar Intanet Mai Inganci
  • Sin Da Japan Da Koriya Ta Kudu Sun Sake Karfafa Huldar Diflomasiyya

Duk da cewa lokaci ne mai muhimmanci, ina ganin duniya ta yi sa’a da samun kasar Sin a matsayin shugabar kwamitin a wannan lokaci, kasancewarta mai nuna halin dattako da sanin ya kamata. Na yi imanin cewa, bisa halinta da ma matsayin da ta dauka tun bayan fara rikicin na kin daukar wani bangare da kuma yadda ta shiga aka dama da ita, har da kada kuri’ar amincewa da kudurin tsagaita bude wuta a lokacin zama na gaggawa da MDD ta yi kan batun rikicin, kasar Sin za ta sauke nauyin dake wuyanta a matsayin babbar kasa.

Tun da dadewa, kasar Sin ta kasance mai neman warware rikicin na Palasdinu cikin lumana kuma bisa adalci ta yadda za a samu zaman lafiya mai dorewa a yankin. Don haka, babu wata kasa da ta cancanci jagorantar batun warware rikicin kamar Sin. Kuma muna da Yakini a wannan karo yayin da take jagorantar kwamitin sulhu, za ta yi iyakar kokarin ganin an tabbatar da adalci kuma an lalubo bakin zaren.

Kamar yadda a kwanakin baya wakilan kasashen Larabawa da na musulmi suka kawo ziyara kasar Sin dangane da batun, saboda kwarin gwiwar da suke da shi kan kasar na karfin warware batun, na tabbata haka sauran al’ummomin duniya masu kaunar zaman lafiya ke da yakinin kasar Sin za ta iya yin kyakkywan tasiri wajen tabbatar da an tsagaita bude wuta da samun maslaha.

LABARAI MASU NASABA

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

Duk da cewa, rikicin Palasdinu da Isra’ila ba abu ne da za a iya warware shi cikin wata guda na wa’adin kasar Sin ba, na tabbata, kamar a ko da yaushe, hangen nesa da sanin ya kamata da ma kaifin basirar kasar Sin za su kaita ga share fage ko saita alkiblar shawo kan rikicin da samar da hanyar zaman lafiya.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 
Daga Birnin Sin

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

November 10, 2025
Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

November 10, 2025
Next Post
Rikicin Yola: Ba Yaki Mu Ke Yi Da Sojoji Ba – Sufeton ‘Yansanda

Rikicin Yola: Ba Yaki Mu Ke Yi Da Sojoji Ba - Sufeton 'Yansanda

LABARAI MASU NASABA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Yi Barazanar Maka BBC A Kotu Tare Da Neman Diyyar $1bn

November 11, 2025
Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 A Ƙauyen Katsina

November 11, 2025
An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

November 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025
Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

November 10, 2025
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

November 10, 2025
Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

November 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.