• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Kin Gaskiya…

by CMG Hausa
2 years ago
South Korean fishermen stage a rally against the planned release of treated radioactive water from the wrecked Fukushima nuclear power plant, in front of the National Assembly in Seoul, South Korea, Monday, June 12, 2023. (AP Photo/Ahn Young-joon)

South Korean fishermen stage a rally against the planned release of treated radioactive water from the wrecked Fukushima nuclear power plant, in front of the National Assembly in Seoul, South Korea, Monday, June 12, 2023. (AP Photo/Ahn Young-joon)

Da alamun dai Japan ba ta hakura da shirinta na zubar da ruwan dagwalon nukiliya a cikin teku ba, duk da kiraye-kiraye da sassan kasa da kasa ke mata kan illar da hakan ga rayuwar daukacin bil-Adama.

Wannan ne ma ya sa kasar Sin ta sake ankarar da Japan din, da ta yi la’akari da kimiya, ta kaucewa aukuwar hadari da ma yin komai ba tare da wata rufa-rufa ba game da shirin nata.

  • INEC Za Ta Gurfanar Da Wadanda Ake Zargi Da Aikata Laifukan Zabe

Kasar Sin da ragowar kasashen duniya, na fatan Japan za ta yi matukar la’akari da damuwar sassan kasa da kasa da ma al’ummarta a cikin guda. Wani abin takaici shi ne akwai rahotannin kafofin watsa labarai dake nuna cewa, Japan ta shawo hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya game da rahotonta na karshe, mai nasaba da tsarin Japan din na zubar da ruwan dagwalon nukiliya a cikin teku, lamarin da ya kara sanya kasashen duniya cikin damuwa, domin rahoton hukumar ba ya nufin an amince Japan ta zubar da ruwan dagwalon nukiliyar a cikin teku. Wai yaro bar murna karenka ya kama zaki.

Ya kamata Japan ta fahimci cewa, zubar da ruwan dagwalon nukiliyar a cikin teku, daidai yake da dawo da hadarin illar nukiliya ga daukacin bil-Adama, kuma wannan matakin da kasar Japan ta dauka, ya saba wa muradun da’a na kasa da kasa, da dokokin kasa da kasa kamar yarjejeniyar MDD kan dokar teku, da yarjejeniyar London ta hana gurbatar ruwa ta hanyar zubar da sharar gida da sauran al’amura.

Masharhanta dai na bayyana cewa, abu mafi fa’ida shi ne Japan, da ta dakatar da shirinta na zubar da ruwan dagwalon a cikin teku, maimakon haka ta sarrafa shi ta hanyar kimiyya, aminci da gaskiya, ta kuma hada kai da hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa IAEA, don aiwatar da matakan da suka dace game da tsarin sa ido na kasa da kasa na dogon lokaci, wanda zai shafi makwabtan Japan da sauran masu ruwa da tsaki ba tare da bata lokaci ba. Haka kuma ya wajaba hukumar IAEA ta gabatar da rahotonta na nazari bisa goyon bayan kimiya da tarihi, maimakon amincewa da matsayar Japan na zubar da ruwan dagwalon nukiliya a cikin teku. Ya dace Japan ta fahimci cewa, bayan kin gaskiya fa, sai bata, kuma tsalla daya ake yi a fada rijiya, amma sai an yi dubu kafin a fito.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

Don haka, Japan tana da sauran lokaci na gyara wannan batu, don gudun dan da na sani….

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba
Daga Birnin Sin

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
Next Post
Kotu Ta Aike Da Wani Direban Adaidaita Sahu Gidan Gyaran Hali Kan Laifin Kisa A Adamawa

Kotu Ta Aike Da Wani Direban Adaidaita Sahu Gidan Gyaran Hali Kan Laifin Kisa A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.