ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Kin Gaskiya…

by CMG Hausa
3 years ago
South Korean fishermen stage a rally against the planned release of treated radioactive water from the wrecked Fukushima nuclear power plant, in front of the National Assembly in Seoul, South Korea, Monday, June 12, 2023. (AP Photo/Ahn Young-joon)

South Korean fishermen stage a rally against the planned release of treated radioactive water from the wrecked Fukushima nuclear power plant, in front of the National Assembly in Seoul, South Korea, Monday, June 12, 2023. (AP Photo/Ahn Young-joon)

Da alamun dai Japan ba ta hakura da shirinta na zubar da ruwan dagwalon nukiliya a cikin teku ba, duk da kiraye-kiraye da sassan kasa da kasa ke mata kan illar da hakan ga rayuwar daukacin bil-Adama.

Wannan ne ma ya sa kasar Sin ta sake ankarar da Japan din, da ta yi la’akari da kimiya, ta kaucewa aukuwar hadari da ma yin komai ba tare da wata rufa-rufa ba game da shirin nata.

  • INEC Za Ta Gurfanar Da Wadanda Ake Zargi Da Aikata Laifukan Zabe

Kasar Sin da ragowar kasashen duniya, na fatan Japan za ta yi matukar la’akari da damuwar sassan kasa da kasa da ma al’ummarta a cikin guda. Wani abin takaici shi ne akwai rahotannin kafofin watsa labarai dake nuna cewa, Japan ta shawo hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya game da rahotonta na karshe, mai nasaba da tsarin Japan din na zubar da ruwan dagwalon nukiliya a cikin teku, lamarin da ya kara sanya kasashen duniya cikin damuwa, domin rahoton hukumar ba ya nufin an amince Japan ta zubar da ruwan dagwalon nukiliyar a cikin teku. Wai yaro bar murna karenka ya kama zaki.

ADVERTISEMENT

Ya kamata Japan ta fahimci cewa, zubar da ruwan dagwalon nukiliyar a cikin teku, daidai yake da dawo da hadarin illar nukiliya ga daukacin bil-Adama, kuma wannan matakin da kasar Japan ta dauka, ya saba wa muradun da’a na kasa da kasa, da dokokin kasa da kasa kamar yarjejeniyar MDD kan dokar teku, da yarjejeniyar London ta hana gurbatar ruwa ta hanyar zubar da sharar gida da sauran al’amura.

Masharhanta dai na bayyana cewa, abu mafi fa’ida shi ne Japan, da ta dakatar da shirinta na zubar da ruwan dagwalon a cikin teku, maimakon haka ta sarrafa shi ta hanyar kimiyya, aminci da gaskiya, ta kuma hada kai da hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa IAEA, don aiwatar da matakan da suka dace game da tsarin sa ido na kasa da kasa na dogon lokaci, wanda zai shafi makwabtan Japan da sauran masu ruwa da tsaki ba tare da bata lokaci ba. Haka kuma ya wajaba hukumar IAEA ta gabatar da rahotonta na nazari bisa goyon bayan kimiya da tarihi, maimakon amincewa da matsayar Japan na zubar da ruwan dagwalon nukiliya a cikin teku. Ya dace Japan ta fahimci cewa, bayan kin gaskiya fa, sai bata, kuma tsalla daya ake yi a fada rijiya, amma sai an yi dubu kafin a fito.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Don haka, Japan tana da sauran lokaci na gyara wannan batu, don gudun dan da na sani….

Japan
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
Daga Birnin Sin

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Next Post
Kotu Ta Aike Da Wani Direban Adaidaita Sahu Gidan Gyaran Hali Kan Laifin Kisa A Adamawa

Kotu Ta Aike Da Wani Direban Adaidaita Sahu Gidan Gyaran Hali Kan Laifin Kisa A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.