• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Tube Wa Mahaifinta Rawani, Kwamishina Ta Yi Murabus A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Bayan Tube Wa Mahaifinta Rawani, Kwamishina Ta Yi Murabus A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasa da ‘yan awanni da cire mahaifinta daga sarautar Wazirin Bauchi, Kwamishiniyar ma’aikatar kasuwanci da masana’antu ta jihar Bauchi, Hajiya Sa’adatu Bello Kirfi ta yi murabus daga mukaminta. 

 

Sa’adatu a wata wasikar da ta aike wa gwamnan Jihar Bauchi Bala Muhammad mai kwanan wata 4 ga Janairun 2023 ta ce ajiye aikin nata ya fara aiki ne nan take.

  • An Tsige Wazirin Masarautar Bauchi Kan Rashin Yi Wa Gwamna Biyayya

Daga bisani ta gode wa gwamnan Jihar a bisa ba ta damar zama daga cikin mambobin Majalisar zartaswa ta jihar.

 

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Duk da ya ke dai ba ta yi bayanin dalilan da suka sanya ta ajiye mukamin nata ba, ana ganin bai rasa nasaba da korar mahaifinta Alhaji Muhammad Bello Kirfi daga Sarautarsa ta Wazirin Bauchi ba bisa abun da aka misalta rashin biyayya da rashin mutunta gwamnan Jihar Bauchi Bala Muhammad da aka sameshi da yi.

 

A wasikar tsige Bello Kirfi daga mambar Majalisar masarautar ta Bauchi mai dauke da kwanan wata Talata 3 ga watan Janairun 2023 dauke da sanya hannun sakataren masarautar, Alhaji Shehu Mudi Muhammad da wakilinmu ya ci karo da ita.

 

Wani bari na wasikar na cewa, “An umarceni da na koma ga wasikar da aka samu daga ma’aikatar kananan hukumomi da kula da harkokin masarautun gargajiya mai lamba MLG/LG/S/72/T da ke dauke da kwanan wata 30 ga watan Disamban 2022.”

 

“Wasikar na kunshe da cewa ba ka biyayya da mutunta mai girma gwamnan Jihar Bauchi da Gwamnati. Kan hakan an umarci a cire ka nan take.

 

“Bisa bayanan da suke a sama, an cireka daga ofis a matsayin Wazirin Bauchi kuma mamba a cikin Majalisar masarautar Bauchi”.

 

Alhaji Shehu Mudi Muhammad daga bisani ya yi wa korarren Wazirin Bauchi fatan alkairi a rayuwarsa ta gaba.

 

LEADERSHIP Hausa ta yi tilawar cewa shi dai Wazirin Bauchi, Alhaji Muhammad Bello Kirfi an taba dakatar da shi daga sarautarsa a zamanin mulki gwamna Muhammad Abdullahi Abubakar wanda Sarkin Bauchi Dakta Rilwanu Sulaiman Adamu ya yi a watan Maris na 2017.

 

Bayan da gwamna Bala Muhammad Abdulkadir ya zama gwamna a 2019 ya shiga ya fita har aka samu nasarar sake dawowa Muhammad Bello Kirfi da Sarautarsa, yanzu kuma an koreshi gaba daya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Al’ajabi: Yadda Mata Da Miji Suka Rasu Akan Gadon Aurensu A Kano

Next Post

Mutum 18 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Bauchi

Related

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara
Tsaro

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

15 minutes ago
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa
Labarai

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

45 minutes ago
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya
Labarai

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

2 hours ago
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC
Labarai

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

3 hours ago
Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya
Labarai

Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

6 hours ago
Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa
Labarai

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

7 hours ago
Next Post
Mutum 18 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Bauchi

Mutum 18 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

October 5, 2025
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

October 5, 2025
CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

October 5, 2025
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

October 5, 2025
Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

October 5, 2025
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

October 5, 2025
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

October 5, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

October 5, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.