• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Tube Wa Mahaifinta Rawani, Kwamishina Ta Yi Murabus A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Bayan Tube Wa Mahaifinta Rawani, Kwamishina Ta Yi Murabus A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasa da ‘yan awanni da cire mahaifinta daga sarautar Wazirin Bauchi, Kwamishiniyar ma’aikatar kasuwanci da masana’antu ta jihar Bauchi, Hajiya Sa’adatu Bello Kirfi ta yi murabus daga mukaminta. 

 

Sa’adatu a wata wasikar da ta aike wa gwamnan Jihar Bauchi Bala Muhammad mai kwanan wata 4 ga Janairun 2023 ta ce ajiye aikin nata ya fara aiki ne nan take.

  • An Tsige Wazirin Masarautar Bauchi Kan Rashin Yi Wa Gwamna Biyayya

Daga bisani ta gode wa gwamnan Jihar a bisa ba ta damar zama daga cikin mambobin Majalisar zartaswa ta jihar.

 

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Wanke Fayose Daga Zargin Zambar Naira Biliyan 3.3

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Duk da ya ke dai ba ta yi bayanin dalilan da suka sanya ta ajiye mukamin nata ba, ana ganin bai rasa nasaba da korar mahaifinta Alhaji Muhammad Bello Kirfi daga Sarautarsa ta Wazirin Bauchi ba bisa abun da aka misalta rashin biyayya da rashin mutunta gwamnan Jihar Bauchi Bala Muhammad da aka sameshi da yi.

 

A wasikar tsige Bello Kirfi daga mambar Majalisar masarautar ta Bauchi mai dauke da kwanan wata Talata 3 ga watan Janairun 2023 dauke da sanya hannun sakataren masarautar, Alhaji Shehu Mudi Muhammad da wakilinmu ya ci karo da ita.

 

Wani bari na wasikar na cewa, “An umarceni da na koma ga wasikar da aka samu daga ma’aikatar kananan hukumomi da kula da harkokin masarautun gargajiya mai lamba MLG/LG/S/72/T da ke dauke da kwanan wata 30 ga watan Disamban 2022.”

 

“Wasikar na kunshe da cewa ba ka biyayya da mutunta mai girma gwamnan Jihar Bauchi da Gwamnati. Kan hakan an umarci a cire ka nan take.

 

“Bisa bayanan da suke a sama, an cireka daga ofis a matsayin Wazirin Bauchi kuma mamba a cikin Majalisar masarautar Bauchi”.

 

Alhaji Shehu Mudi Muhammad daga bisani ya yi wa korarren Wazirin Bauchi fatan alkairi a rayuwarsa ta gaba.

 

LEADERSHIP Hausa ta yi tilawar cewa shi dai Wazirin Bauchi, Alhaji Muhammad Bello Kirfi an taba dakatar da shi daga sarautarsa a zamanin mulki gwamna Muhammad Abdullahi Abubakar wanda Sarkin Bauchi Dakta Rilwanu Sulaiman Adamu ya yi a watan Maris na 2017.

 

Bayan da gwamna Bala Muhammad Abdulkadir ya zama gwamna a 2019 ya shiga ya fita har aka samu nasarar sake dawowa Muhammad Bello Kirfi da Sarautarsa, yanzu kuma an koreshi gaba daya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Al’ajabi: Yadda Mata Da Miji Suka Rasu Akan Gadon Aurensu A Kano

Next Post

Mutum 18 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Bauchi

Related

Kotu Ta Wanke Fayose Daga Zargin Zambar Naira Biliyan 3.3
Manyan Labarai

Kotu Ta Wanke Fayose Daga Zargin Zambar Naira Biliyan 3.3

50 minutes ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

2 hours ago
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Labarai

Yara 2 Sun Kuɓuta Bayan Shafe Shekaru 6 A Hannun Boko Haram A Borno

4 hours ago
Kasa Da Wata Biyu Ya Bar Mulki, Shin Ko Buhari Ya Cika Wa ‘Yan Nijeriya Alkawarin Da Ya Yi Mu Su?
Manyan Labarai

EU, Turkiyya Da Sauran Ƙasashe Sun Yi Ta’aziyyar Rasuwar Buhari

5 hours ago
Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari
Labarai

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

14 hours ago
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano
Labarai

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

14 hours ago
Next Post
Mutum 18 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Bauchi

Mutum 18 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Wanke Fayose Daga Zargin Zambar Naira Biliyan 3.3

Kotu Ta Wanke Fayose Daga Zargin Zambar Naira Biliyan 3.3

July 16, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

July 16, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Yara 2 Sun Kuɓuta Bayan Shafe Shekaru 6 A Hannun Boko Haram A Borno

July 16, 2025
Kasa Da Wata Biyu Ya Bar Mulki, Shin Ko Buhari Ya Cika Wa ‘Yan Nijeriya Alkawarin Da Ya Yi Mu Su?

EU, Turkiyya Da Sauran Ƙasashe Sun Yi Ta’aziyyar Rasuwar Buhari

July 16, 2025
Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

July 15, 2025
Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 15, 2025
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

July 15, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.