• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayar Da Tallafin Wutar Lantarki Kaso 85 na Kara Nuna Tinubu Mai Kishin Jama’a Ne – Minista

by Sulaiman
2 years ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce, ci gaba da bayar da tallafin wutar lantarki kashi 85 cikin 100 da gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ke yi ya ƙara nuna gwamnatin a matsayin dimokiraɗiyya mai son jama’a.

Ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a a jawabin sa na buɗe Taron Ministoci Karo na 4 a Cibiyar ‘Yan Jaridu ta Ƙasa da ke Abuja.

  • 2023: Manyan Jiragen Ruwa 75,000 Suka Yi Hada-hada A Tashar Lekki
  • Yau Za A Yi Mugun Zafi Mai Haɗari A Abuja, Sakkwato, Kano Da Kogi, In Ji NiMet

Ministan ya ce: “A kwanan baya, Gwamnatin Tarayya ta fitar da wani tsari na cigaba a fannin samar da wutar lantarki, wanda ke da nufin bunƙasa wadatar wutar lantarki ga ɗaukacin ‘yan Nijeriya.

“Wani muhimmin al’amari na wannan tsarin shi ne gwamnatin Tinubu na ci gaba da bayar da tallafin wutar lantarki ga kashi 85 na masu amfani da wutar lantarki a Nijeriya, wanda hakan ya sake tabbatar da matsayin gwamnatin dimokaradiyya mai son jama’a tare da yin ƙarin kuɗin wutar lantarki ga kashi 15 na masu amfani da wutar lantarki kawai.”

Tun da farko, Ministan ya bayyana nasarorin da gwamnatin Shugaban Ƙasa Tinubu ta samu a baya-bayan nan. A cewar Idris, “Tun bayan ganawar da muka yi da ku (’yan jarida) na baya-bayan nan an samu gagarumar nasara a tattalin arziƙinmu, kasancewar dukkanmu shaida ne kan yadda ta hanyar aiwatar da wasu sauye-sauye na tattalin arziƙi, kasuwar canjin kuɗaɗen ƙasar waje ta daidaita, sannan kuma naira yana samun ƙarfi kullum.

LABARAI MASU NASABA

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

“Kafa Majalisar Daidaita Tattalin Arziƙi da Tawagar Gudanar da Tattalin Arziƙi na Shugaban Ƙasa na kwanan nan ya jaddada ƙudirin Shugaban Ƙasa don samar da wani tsari mai muhimmanci na gudanar da tattalin arziƙi wanda ke yin amfani da ƙwarewa da fahimtar manyan masu ruwa da tsaki daga ɓangarorin gwamnati da masu zaman kansu. Waɗannan ƙungiyoyin za su zama dandamali don tattaunawa mai ƙarfi, bincike, da yanke shawara don haɓaka ci gaban tattalin arziƙi mai ɗorewa, samar da ayyukan yi, da wadata ga dukkan ‘yan Nijeriya.

“Ƙaddamar da Asusun Raya Gine-gine na Sabunta Fata (RHIDF) yana da niyyar tara kusan naira tiriliyan 20 don saka hannun jari a sassa masu muhimmanci kamar su tattalin arziƙi, sufuri, noma, da Fasahar Sadarwar Bayanai (ICT) da sauransu.

“Asusun yana neman tallafawa ayyukan da ke haɓaka ci gaba, samar da guraben aikin yi, da haɓaka fitar da kayayyaki zuwa ketare.”

Idris ya ƙara da cewa, “Ayyukan da asusun zai sa a gaba sun haɗa da gina babbar hanyar Legas zuwa Calabar da aka fara kwanan nan, titin Sokoto zuwa Badagry, Legas zuwa Kano, hanyar jirgin ƙasa na Gabas da zamanantar da tashoshin jiragen ruwa da na jiragen sama a faɗin ƙasar.

“Don faɗaɗa hanyoyin samun ilimi a matsayin makamin yaƙi da talauci, Shugaban Ƙasa ya sanya hannu kan ƙudirin dokar Lamunin Ɗalibai ta 2015, ta zama doka. Wannan yunƙurin ya wuce doka kawai – hanya ce ta juyin juya hali don kafa tsari na dindindin wanda zai tallafa wa neman ilimi daga matasanmu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa
Manyan Labarai

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa
Manyan Labarai

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba
Manyan Labarai

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Next Post
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC

Sojojin Nijeriya Na Da Kwarewar Da Za Su Kawo Karshen Matsalar Tsaro - Kwankwaso

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.