• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bidiyon Dala: Gwamnatin Kano Ta Fara Bincike Akan Ganduje

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
Bidiyon Dala: Gwamnatin Kano Ta Fara Bincike Akan Ganduje
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Karbar Koke da Yaki da Cin Hancin da Rashawa ta Jihar Kano (PCACC), ta kaddamar da fara bincike akan tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje kan zargin karbar dala da wani faifan bidiyo ya nuna yana karba.

Shugaban hukumar, Muhuyi Magaji Rimingado, ya bayyana hakan a lokacin da ya tabbatar da cafke tsohon kwamishinan jihar, Injiniya Idris Wada Saleh akan zargin badakalar dala biliyan daya.

  • Jihohi 14 Da Za Su Fuskanci Ambaliyar Ruwa —NEMA
  • Kotu Ta Tabbatar Da Korar Goje Daga Jami’yyar APC

Muhuyi wanda ya sanar da hakan a taron manema labarai a jiya Talata ya ce a yanzu haka hukumar ta kaddamar da fara bincike wanda kuma ta karbi rahoton binciken faifan bidiyon karbar dalar da ake zargin Ganduje.

A wani shirin tattaunawa da gidan talabijin na Trust, Muhyi ya lashi Takobin bude faifan bidiyon da suka nuna Ganduje yana karbar daloli yana zuba wasu a cikin aljihunsa a matsayin cin hanci daga wajen wani dan kwangila, wanda Ganduje ya karyata hakan.

A cewarsa, “babu wata kotu da ta taka mana birki kan wannan matakan da muke dauka.”

Labarai Masu Nasaba

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

Shugaban ya kara da cewa, hukumar ta kuma rubutawa EFCC wasikar neman yin hadaka don yin binciken tare da ganin an hukunta Ganduje.

A cewarsa, ganin cewa hukumar ba ta riga ta samu wata amsa daga wajen EFCC kan wasikar da ta aika mata ba, PCACC za ta gudanar da nata binciken ta hanyar janyo sauran hukomomi cikin binciken.

Da yake yin tsokaci akan zargin badakalar kama tsohon kwamishinan kan almundahanar Naira biliyan daya, shugaban ya ce tsohon kwamishinan ya yi hakan ne, da sunan yin gyaran wasu hanyoyin jihar a cikin mako daya da gwaman jihar ke sihirin sauka daga mulki.

Ya ce, an kuma kama Manajin Darakta na hukumar gyaran hanyoyi na jihar (KARMA) tare da babban sakataren hukumar BPP na jihar, Mustapha Madaki Huguma da Daraktan kudi da kuma Daraktan sashen bincike da tsare-tsare na jihar a ranar Litinin.

Ya ce, kudin da ake magana akai an fitar da su an kuma turawa kamfanonin an fitar da su ne a ranar 25 ga watan Afirilu.

A wata sabuwa kuwa, kotun majistare a jihar Kano, ta bayar da umarnin ajiye tsohon kwamishinan har zuwa kwanaki 12 kafin a kammala bincike.

An kai shi gaban kotu ne a ranar Talata kan tuhuma biyu da suka hada sauya bayanai da kuma yin cuta.

Lauya mai gabatar da kara, Salisu Tahir kuma Mataimakin Darakta a hukumar PCACC ya shaida wa kotun cewa, wanda ake tuhumar a 2023 ya fitar da kudin ga kamfanin Arafat Construction da kamfanin No Stone Construction da kuma ga kamfanin Multi Resources don gyran hanyoyi 30 a cikin birnin Kano wanda kuma ba a gudanar da aikin ba.

Ya kuma bukaci da a kai ajiyar wanda kotun ke tuhuma na kwana 14, sai dai wanda ake tuhumar bai amsa laifinsa ba.

Mustapha Idris, wanda yake tsayawa wanda ake tuhuma ya shawarci kotun da ta yi amfani da sashe na 35 da na 6 na kundin tsarin mulkin Nijeriya don a bayar da belinsa.

Amma a hukuncin da alkalin kotun majistaren mai shari’a Tijjani Sale-Minjibir ya yanke, ya bayar da umarnin a ajiye shi har zuwa kwanaki 12 tare da ba shi kular da ta kamata.

Kotun ta dage sauraren karar zuwa ranar 14 ga watan Yuli.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bidiyon DalaBincikeGandujekanoPCACC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jihohi 14 Da Za Su Fuskanci Ambaliyar Ruwa —NEMA

Next Post

Kotu Ta Daure Matashi Kan Guntule Wa Abokinsa Hannu A Bauchi

Related

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya
Labarai

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

7 hours ago
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano
Labarai

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

8 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari
Labarai

Za A Dinga Tunawa Da Buhari A Matsayin Waliyyi A Siyasar Nijeriya —Dakta Zangina

9 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

9 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas

10 hours ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

10 hours ago
Next Post
Kotu Ta Daure Basarake Shekaru 15 Saboda Garkuwa Da Kansa

Kotu Ta Daure Matashi Kan Guntule Wa Abokinsa Hannu A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.