• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bidiyon Dala: Gwamnatin Kano Ta Fara Bincike Akan Ganduje

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
Bidiyon Dala: Gwamnatin Kano Ta Fara Bincike Akan Ganduje
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Karbar Koke da Yaki da Cin Hancin da Rashawa ta Jihar Kano (PCACC), ta kaddamar da fara bincike akan tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje kan zargin karbar dala da wani faifan bidiyo ya nuna yana karba.

Shugaban hukumar, Muhuyi Magaji Rimingado, ya bayyana hakan a lokacin da ya tabbatar da cafke tsohon kwamishinan jihar, Injiniya Idris Wada Saleh akan zargin badakalar dala biliyan daya.

  • Jihohi 14 Da Za Su Fuskanci Ambaliyar Ruwa —NEMA
  • Kotu Ta Tabbatar Da Korar Goje Daga Jami’yyar APC

Muhuyi wanda ya sanar da hakan a taron manema labarai a jiya Talata ya ce a yanzu haka hukumar ta kaddamar da fara bincike wanda kuma ta karbi rahoton binciken faifan bidiyon karbar dalar da ake zargin Ganduje.

A wani shirin tattaunawa da gidan talabijin na Trust, Muhyi ya lashi Takobin bude faifan bidiyon da suka nuna Ganduje yana karbar daloli yana zuba wasu a cikin aljihunsa a matsayin cin hanci daga wajen wani dan kwangila, wanda Ganduje ya karyata hakan.

A cewarsa, “babu wata kotu da ta taka mana birki kan wannan matakan da muke dauka.”

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Shugaban ya kara da cewa, hukumar ta kuma rubutawa EFCC wasikar neman yin hadaka don yin binciken tare da ganin an hukunta Ganduje.

A cewarsa, ganin cewa hukumar ba ta riga ta samu wata amsa daga wajen EFCC kan wasikar da ta aika mata ba, PCACC za ta gudanar da nata binciken ta hanyar janyo sauran hukomomi cikin binciken.

Da yake yin tsokaci akan zargin badakalar kama tsohon kwamishinan kan almundahanar Naira biliyan daya, shugaban ya ce tsohon kwamishinan ya yi hakan ne, da sunan yin gyaran wasu hanyoyin jihar a cikin mako daya da gwaman jihar ke sihirin sauka daga mulki.

Ya ce, an kuma kama Manajin Darakta na hukumar gyaran hanyoyi na jihar (KARMA) tare da babban sakataren hukumar BPP na jihar, Mustapha Madaki Huguma da Daraktan kudi da kuma Daraktan sashen bincike da tsare-tsare na jihar a ranar Litinin.

Ya ce, kudin da ake magana akai an fitar da su an kuma turawa kamfanonin an fitar da su ne a ranar 25 ga watan Afirilu.

A wata sabuwa kuwa, kotun majistare a jihar Kano, ta bayar da umarnin ajiye tsohon kwamishinan har zuwa kwanaki 12 kafin a kammala bincike.

An kai shi gaban kotu ne a ranar Talata kan tuhuma biyu da suka hada sauya bayanai da kuma yin cuta.

Lauya mai gabatar da kara, Salisu Tahir kuma Mataimakin Darakta a hukumar PCACC ya shaida wa kotun cewa, wanda ake tuhumar a 2023 ya fitar da kudin ga kamfanin Arafat Construction da kamfanin No Stone Construction da kuma ga kamfanin Multi Resources don gyran hanyoyi 30 a cikin birnin Kano wanda kuma ba a gudanar da aikin ba.

Ya kuma bukaci da a kai ajiyar wanda kotun ke tuhuma na kwana 14, sai dai wanda ake tuhumar bai amsa laifinsa ba.

Mustapha Idris, wanda yake tsayawa wanda ake tuhuma ya shawarci kotun da ta yi amfani da sashe na 35 da na 6 na kundin tsarin mulkin Nijeriya don a bayar da belinsa.

Amma a hukuncin da alkalin kotun majistaren mai shari’a Tijjani Sale-Minjibir ya yanke, ya bayar da umarnin a ajiye shi har zuwa kwanaki 12 tare da ba shi kular da ta kamata.

Kotun ta dage sauraren karar zuwa ranar 14 ga watan Yuli.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bidiyon DalaBincikeGandujekanoPCACC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jihohi 14 Da Za Su Fuskanci Ambaliyar Ruwa —NEMA

Next Post

Kotu Ta Daure Matashi Kan Guntule Wa Abokinsa Hannu A Bauchi

Related

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Manyan Labarai

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

44 minutes ago
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC
Labarai

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

10 hours ago
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19
Da ɗumi-ɗuminsa

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

11 hours ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Da ɗumi-ɗuminsa

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

12 hours ago
Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar

13 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Da ɗumi-ɗuminsa

Lauyoyin Majalisar Dattawa Sun Ƙaryata Natasha Kan Cewa Kotu Ta Ce Ta Koma Bakin Aiki

15 hours ago
Next Post
Kotu Ta Daure Basarake Shekaru 15 Saboda Garkuwa Da Kansa

Kotu Ta Daure Matashi Kan Guntule Wa Abokinsa Hannu A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

July 7, 2025
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

July 7, 2025
Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

July 7, 2025
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.