ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bidiyon Dala: Gwamnatin Kano Ta Fara Bincike Akan Ganduje

by Abubakar Abba
3 years ago
Ganduje

Hukumar Karbar Koke da Yaki da Cin Hancin da Rashawa ta Jihar Kano (PCACC), ta kaddamar da fara bincike akan tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje kan zargin karbar dala da wani faifan bidiyo ya nuna yana karba.

Shugaban hukumar, Muhuyi Magaji Rimingado, ya bayyana hakan a lokacin da ya tabbatar da cafke tsohon kwamishinan jihar, Injiniya Idris Wada Saleh akan zargin badakalar dala biliyan daya.

  • Jihohi 14 Da Za Su Fuskanci Ambaliyar Ruwa —NEMA
  • Kotu Ta Tabbatar Da Korar Goje Daga Jami’yyar APC

Muhuyi wanda ya sanar da hakan a taron manema labarai a jiya Talata ya ce a yanzu haka hukumar ta kaddamar da fara bincike wanda kuma ta karbi rahoton binciken faifan bidiyon karbar dalar da ake zargin Ganduje.

ADVERTISEMENT

A wani shirin tattaunawa da gidan talabijin na Trust, Muhyi ya lashi Takobin bude faifan bidiyon da suka nuna Ganduje yana karbar daloli yana zuba wasu a cikin aljihunsa a matsayin cin hanci daga wajen wani dan kwangila, wanda Ganduje ya karyata hakan.

A cewarsa, “babu wata kotu da ta taka mana birki kan wannan matakan da muke dauka.”

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

Shugaban ya kara da cewa, hukumar ta kuma rubutawa EFCC wasikar neman yin hadaka don yin binciken tare da ganin an hukunta Ganduje.

A cewarsa, ganin cewa hukumar ba ta riga ta samu wata amsa daga wajen EFCC kan wasikar da ta aika mata ba, PCACC za ta gudanar da nata binciken ta hanyar janyo sauran hukomomi cikin binciken.

Da yake yin tsokaci akan zargin badakalar kama tsohon kwamishinan kan almundahanar Naira biliyan daya, shugaban ya ce tsohon kwamishinan ya yi hakan ne, da sunan yin gyaran wasu hanyoyin jihar a cikin mako daya da gwaman jihar ke sihirin sauka daga mulki.

Ya ce, an kuma kama Manajin Darakta na hukumar gyaran hanyoyi na jihar (KARMA) tare da babban sakataren hukumar BPP na jihar, Mustapha Madaki Huguma da Daraktan kudi da kuma Daraktan sashen bincike da tsare-tsare na jihar a ranar Litinin.

Ya ce, kudin da ake magana akai an fitar da su an kuma turawa kamfanonin an fitar da su ne a ranar 25 ga watan Afirilu.

A wata sabuwa kuwa, kotun majistare a jihar Kano, ta bayar da umarnin ajiye tsohon kwamishinan har zuwa kwanaki 12 kafin a kammala bincike.

An kai shi gaban kotu ne a ranar Talata kan tuhuma biyu da suka hada sauya bayanai da kuma yin cuta.

Lauya mai gabatar da kara, Salisu Tahir kuma Mataimakin Darakta a hukumar PCACC ya shaida wa kotun cewa, wanda ake tuhumar a 2023 ya fitar da kudin ga kamfanin Arafat Construction da kamfanin No Stone Construction da kuma ga kamfanin Multi Resources don gyran hanyoyi 30 a cikin birnin Kano wanda kuma ba a gudanar da aikin ba.

Ya kuma bukaci da a kai ajiyar wanda kotun ke tuhuma na kwana 14, sai dai wanda ake tuhumar bai amsa laifinsa ba.

Mustapha Idris, wanda yake tsayawa wanda ake tuhuma ya shawarci kotun da ta yi amfani da sashe na 35 da na 6 na kundin tsarin mulkin Nijeriya don a bayar da belinsa.

Amma a hukuncin da alkalin kotun majistaren mai shari’a Tijjani Sale-Minjibir ya yanke, ya bayar da umarnin a ajiye shi har zuwa kwanaki 12 tare da ba shi kular da ta kamata.

Kotun ta dage sauraren karar zuwa ranar 14 ga watan Yuli.

Ganduje
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Next Post
Kotu Ta Daure Basarake Shekaru 15 Saboda Garkuwa Da Kansa

Kotu Ta Daure Matashi Kan Guntule Wa Abokinsa Hannu A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.