• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin CIIE Ya Sa Kayayyakin Kasashen Afirka Samun Karbuwa

by Sulaiman
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
CIIE
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Lahadi, an bude bikin baje kolin kayayyakin kasa da kasa da ake shigowa da su kasar Sin (CIIE) karo na 6 a birnin Shanghai na kasar Sin. 

Bisa matsayinsa na wani muhimmin bikin da ake tallata kayayyaki, da kulla huldar ciniki, bikin CIIE na ta samun karbuwa tsakanin ‘yan kasuwar kasashen Afirka. A wajen biki na wannan karo, an kawo hulunan ciyayi kirar kasar Togo, da waken koko na kasar Zimbabwe, da ridi na kasar Mali, da kashu din kasar Guinea-Bissau, da abarbar kasar Benin, da duwatsu masu kunshe da ma’adinai na kasar Afirka ta Kudu, da dai sauransu. Wasu kamfanoni 6 na kasar Najeriya ma suna cikin mahalarta bikin baje kolin, inda suka nuna wasu lu’u-lu’u, da amfanin gona na musamman na Najeriya.

  • Yadda Bikin CIIE Ya Inganta Ci Gaban Sin Da Sassan Kasa Da Kasa
  • Yadda Bikin CIIE Ya Inganta Ci Gaban Sin Da Sassan Kasa Da Kasa

Sai dai daya daga cikin kayayyakin da suka fi samun karbuwa wajen bikin CIIE na wannan karo, shi ne wani nau’in abarba da ake kiranta “Burodi mai zaki” ta kasar Benin. Cikin abarbar yana da launin fari, kana yana kunshe da dimbin ruwa mai zaki. Duk wanda ya sha abarbar sai ya yabe ta.

Bisa bikin CIIE na wannan karo, Sinawa sun fara sanin wannan nau’in abarba a karon farko. A nasa bangare, Simon Adovelande, jakadan kasar Benin a kasar Sin, ya nuna kyakkyawan fata game da ci gaban kasarsa ta bangaren samar da abarba, ganin yadda wannan nau’in ’ya’yan itatuwa ke samun karbuwa sosai a kasar Sin. Ko da yake kasar Benin ta kan samar da abarba kimanin ton dubu 400 a duk shekara, wadanda ta fi fitarwa zuwa kasashen Turai da na Afirka, amma Adovelande yana sa ran ganin yawan abarbar da kasar Benin ke fitarwa zuwa kasar Sin kacal ta kai ton dubu 300 a duk shekara, nan ba da dadewa ba.

Cikin kayayyakin kasashen Afirka da aka nuna a wajen bikin CIIE, ban da abarbar kasar Benin da ta fara samun karbuwa, akwai ’ya’yan itatuwa na Avacado din kasar Kenya, wanda tun tuni ya yi farin jini. A shekarar 2018, an nuna daskararren Avacado na kasar Kenya a bikin CIIE a karon farko. Sa’an nan, kasashen Sin da Kenya sun kulla wata yarjejeniya a shekarar 2022, don tabbatar da fitar da Avacado din kasar Kenya zuwa kasar Sin. Daga bisani, Avacado din kasar Kenya ya shiga kasuwannin kasar Sin, da fara zama kayan marmari mai samun karbuwa sosai. Zuwa yanzu, kashi 30% na Avacado din kasar Kenya, an fitar da su zuwa kasar Sin. Kana ana sa ran ganin karuwar jimillar a nan gaba. Ban da haka, hukumomi masu kula da aikin gona na kasar Kenya sun kiyasta cewa, manoman Avacado na kasar Kenya sun samu karuwar kudin shiga da ta kai kashi 30% zuwa 50%, ta hanyar fitar da Avacado zuwa kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Bikin CIIE shi ne na farko a duniya da ya mai da hankali a kan baje kolin kayayyakin da ake shigarwa da su, wanda a kan kaddamar da shi a farkon watan Nuwamban kowace shekara. A bana, an samu manyan baki mahalarta taron da suka zo daga kasashe da yankuna, da kungiyoyin kasa da kasa, har 154. Kana a shekarar 2022, kasar Sin ta shigo da kayayyakin da darajarsu ta kai dalar Amukra tiriliyan 2.7, adadin da ya kusan kai kashi 11% na dukkan kayayyakin da ake shigarwa kasuwannin duniya.

Haka zalika, daga watan Janairu zuwa na Satumban bana, darajar hidimomin da kasar Sin ke shigowa da su ta karu da kashi 22.4%, bisa makamancin lokacin bara. Hakika yadda kasar Sin ke neman shigowa da karin kayayyaki daga ketare, zai iya sa kaimi ga aikin samar da kayayyaki, da bangaren samar da guraben aikin yi, da baiwa jama’a karin kudin shiga, a sauran kasashe, gami da daidaita tsarin da ake bi wajen raba kayayyakin da ake bukata don raya masana’antu. Hakan ya yi kama da maganar Christine Lagarde, tsohuwar babbar darektar asusun ba da lamuni na duniya IMF, wadda a yayin bikin CIIE karon farko da ya gudana a shekarar 2018, ta fada, cewa bikin ya nuna yadda kasar Sin take kokarin sauya fasalin aikin ciniki na duniya, wanda zai amfani kasar Sin, gami da daukacin duniya baki daya.

Ban da haka, yadda kayayyakin kasashen Afirka suka fara samun karbuwa a kasuwannin duniya ta bikin CIIE, ya nuna ma’anar bikin da kasar Sin take gudanarwa ga kasashe masu tasowa. A cewar Stephen Kargbo, wakilin kungiyar raya masana’antu ta Majalisar Dinkin Duniya a kasar Sin, dimbin kamfanoni na kasarsa, wato Saliyo, da na sauran kasashe daban daban dake nahiyar Afirka, sun halarci bikin CIIE na bana, inda suka samu damar nuna fasahohi, da kayayyakinsu a wannan muhimmin dandali na kasa da kasa. Ya ce, “Bikin CIIE na kasar Sin ya ba mabambantan kasashe damar more ci gaban tattalin arzikin duniya, kana kasar ba za ta taba barin wani a baya ba.” (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaAsiyaIran
ShareTweetSendShare
Previous Post

CIIE Na Da Matukar Muhimmanci Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Next Post

Gobara Ta Tashi A Shagon Sayar Da Kayan Kamfanin Samsung A Abuja

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

14 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

14 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

16 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

19 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

21 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

22 hours ago
Next Post
Gobara Ta Tashi A Shagon Sayar Da Kayan Kamfanin Samsung A Abuja

Gobara Ta Tashi A Shagon Sayar Da Kayan Kamfanin Samsung A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.