ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Bikin CIIE Ya Inganta Ci Gaban Sin Da Sassan Kasa Da Kasa

by CGTN Hausa
3 years ago
CIIE

Mataimakin shugaban kamfanin Johnson and Johson na Amurka, kuma jagoran kamfanin a kasar Sin Song Weiqun, ya ce ya ji yadda Sin ke nacewa bude kofa ga waje, da kuma sauke nauyin da ke wuyanta na inganta cigaban tattalin arzikin duniya, da hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya tsakanin kasa da kasa. Song ya bayyana hakan ne bayan nazartar wasikar taya murna da shugaban Sin Xi Jinping ta gabatar ga bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin ko CIIE karo na shida, inda ya kara da cewa, wasikar ta karfafa gwiwar kamfanin Johnson and Johson wajen ci gaba da neman samun bunkasuwa a kasar Sin.

Shekarar bana ita ce ta cika shekaru 45 da Sin ta gabatar da manufofin bude kofa ga kasashen waje da yin gyare-gyare a gida, kuma ta cika shekaru 10 da gabatar da shawarar “Ziri daya da hanya daya”. A wannan shekara mai ma’anar musamman ne kuma ake gudanar da bikin CIIE karo na shida.

  • Baje Kolin CIIE Ya Samu Yabo Daga Sassan Kasa Da Kasa A Matsayin Dandalin Bunkasa Hadin Gwiwa Da Ci Gaba
  • An Bude Bikin CIIE A Shanghai

Yadda kamfanonin kasa da kasa masu dimbin yawa suka shiga bikin CIIE na bana bisa shirin da aka tsara, ya shaida kokarin kasar Sin na cika alkawarinta da kara bude kofarta ga kasashen waje. A yayin bikin CIIE na wannan karo, bangaren Sin ya fitar da jerin manufofi, wadanda suka hada da habaka shigo da kayayyaki daga ketare, da kafa yankin gwajin cinikayya maras shige ko FTZ da sauransu, lamarin da zai taimaka wa kamfanonin kasa da kasa wajen kara samun cigaba a Sin, kana zai shaida yadda bikin CIIE ke bayar da gudummawa wajen inganta matakin bude kofa mai babban matsayi.

ADVERTISEMENT

Bikin CIIE dandamali ne na cudanyar sassa daban daban na duniya. Kuma a nan gaba, bikin zai kara samar da hidimomi masu inganci da zai amfani kasa da kasa, lamarin da ke nuna cewa, Sin za ta tsaya tsayin daka kan ra’ayin kasancewar bangarori daban daban, da nuna adawa da ra’ayoyin rufe kasa, da neman raba-gari da sauran kasashe. Cikin sahihanci, Sin za ta taimakawa sassan kasa da kasa wajen samun cigaba, tare da raya tsarin tattalin arzikin duniya mai salon bude kofa ga juna.

Ko shakka babu baje kolin CIIE ya kawo kwarin gwiwa da karfi ga duniya, a wannan yanayin da ake ciki na barkewar rikice-rikice tsakanin bangarori daban daban, da daukar matakai a makare, da kuma tabarbarewar tattalin arzikin duniya. (Safiyah Ma)

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

CIIE
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
CIIE

CIIE Na Da Matukar Muhimmanci Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.