• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Sallah: Ministan Yaɗa Labarai Ya Nemi ‘Yan Nijeriya Su Dawo Da Kyawawan Dabi’un Da Suka Jingine

by Sulaiman
2 years ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya buƙaci ‘yan Nijeriya da su dawo da kyawawan ɗabi’un da suka rasa tare da ci gaba da addu’o’in samun zaman lafiya da cigaban shugabannin mu da ƙasar mu.

Ya yi wannan kiran ne a Kaduna bayan kammala Sallar Idi.

  • Bayar Da Tallafin Wutar Lantarki Kaso 85 na Kara Nuna Tinubu Mai Kishin Jama’a Ne – Minista
  • Yadda Jami’in Tsaro Ya Bindige Wani Mutum Ana Tsaka Da Sallar Idi A Zamfara

An gudanar da sallar ne a makarantar Kaduna Capital da ke Kaduna a ranar Laraba.

Ministan ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su yi wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu addu’a, tare da amincewa da ƙoƙarin da yake yi na mayar da Nijeriya cikin ƙasashe mafiya inganci a duniya.

Ya ce: “Ana farfaɗo da tattalin arzikin mu, kasuwar canjin kuɗaɗen waje na daidaituwa, ana kuma farfaɗo da harkar noma ta yadda za a samu wadatar abinci ga jama’ar mu. Haƙiƙa yanayin tsaron ƙasar nan ma yana inganta.”

LABARAI MASU NASABA

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Idris ya kuma yi kira ga ‘yan Nijeriya da su yi Allah wadai da duk wasu munanan ayyuka da ‘yan ta’adda ke aikatawa, tare da fatan za su tabbatar da cewa ‘yan Nijeriya sun zauna lafiya.

Haka kuma ya bayyana damuwar sa kan yadda a hankali ɗabi’un ‘yan Nijeriya ke taɓarɓarewa tsawon shekaru.

Ya yi kira ga dukkanin mu da mu haɗa kai mu dawo da waɗannan ɗabi’u domin farfaɗo da kan mu da ƙasar mu.

Minista

Ya kuma buƙaci matasa da su koyi darasi daga abubuwan da suka faru da dattawan su, kuma su guji biye wa sababbin yayi da duniya ke ciki.

“Nijeriya babbar ƙasa ce; Abin da ya kamata mu yi shi ne mu haɗa kai mu tabbatar an rungumi dukkan kyawawan ɗabi’u domin amfanin Nijeriya,” inji shi.

Ministan ya ƙara da cewa: “Domin Nijeriya ta sake zama babbar ƙasa, dole ne mu canza ɗabi’un mu kuma mu ci gaba da nuna duk wasu ɗabi’u da muka koya a cikin watan Ramadan.”

Babban limamin masallacin Makarantar Capital, Imam Abdurrahman, wanda ya jagoranci sallar, ya gabatar da huɗuba, inda ya yi kira ga Musulmi da Kiristoci da su tabbatar da cewa Nijeriya ta zauna lafiya da haɗin kai.

Shi ma ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su dawo da waɗancan ɗabi’u domin su farfaɗo da ƙasar mu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abduljabbar
Labarai

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025
Next Post
Sin Ta Bayyana Rashin Jin Dadi Kan Binciken Da Eu Ta Yiwa Wasu Kamfanonin Sin Masu Samar Da Wasu Hajoji

Sin Ta Bayyana Rashin Jin Dadi Kan Binciken Da Eu Ta Yiwa Wasu Kamfanonin Sin Masu Samar Da Wasu Hajoji

LABARAI MASU NASABA

Abduljabbar

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Kasar Sin: Sin Za Ta Kyautata Matakan Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Kasar Sin: Sin Za Ta Kyautata Matakan Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

October 17, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Zan Tabbatar Ana Tafiyar Da Ayyuka A Tashoshin Jiragen Ruwa A Afrika Ta Yamma —Dantsoho

October 17, 2025
Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

October 17, 2025
peter

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.