• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binciken CGTN Ya Nuna Damuwa Daga Sassan Kasa Da Kasa Game Da Yawaitar Ficewar Amurka Daga Yarjeniyoyin Kasa Da Kasa

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Binciken CGTN Ya Nuna Damuwa Daga Sassan Kasa Da Kasa Game Da Yawaitar Ficewar Amurka Daga Yarjeniyoyin Kasa Da Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sabuwar gwamnatin Amurka, ta yi amfani da kwanakinta na farko a kan karaga wajen zartar da jerin umarnin shugaban kasa, inda ta sanar da ficewar Amurka daga yarjejeniyar sauyin yanayi ta Paris, da hukumar lafiya ta duniya WHO, wanda hakan ya haifar da damuwa tsakanin sassan kasa da kasa. 

Wani binciken jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta kasar Sin ta gudanar, ya nuna cewa, manufar nan ta “Sanya Amurka gaban komai”, ba za ta kai kasar zuwa ga sabon “Lokacin cimma Nasarori” ba, kuma hakan zai iya kara haifar da koma baya ga tsarin gudanar da duniya.

  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Inganta Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa A Taron Davos
  • Kwangilar Tashar Wutar Mambila: Obasanjo Zai Bayar Da Shaida A Kotun Paris Yau

Alkaluman sun nuna cewa, kaso 68.5 bisa dari na masu bayyana ra’ayin na ganin janyewar da sabuwar gwamnatin Amurka ta sanar daga yarjejeniyar Paris, da ficewa daga hukumar kiwon lafiya ta duniya WHO, zai gurgunta hadin gwiwar kasa da kasa, a fannin shawo kan sauyin yanayi, da harkokin kula da lafiyar al’umma. Kaza lika, kaso 77.7 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyinsu sun yi matukar damuwa, cewa akwai yiwuwar matakin ya haifar da wani mummunan misali tsakanin kasashen duniya.

Alal hakika, har kullum Amurka na kallon hukumomin kasa da kasa, da cibiyoyi, da tsare-tsaren gudanar da harkokin duniya ta wata mahanga maras dacewa, da kuma idon kare moriyar kashin kai, tana kallon su a matsayin wasu abubuwa na cimma nasara, da tabbatar da manufarta ta danniya a duniya.

Karkashin manufar “Sanya Amurka gaban komai”, sabuwar gwamnatin kasar na kokarin matsawa hukumomin kasa da kasa lamba, ta yadda dole za su yi biyayya ga Amurka kan batutuwa irin su kafa dokoki, da yadda za a gudanar da cibiyoyi da jagorancin sauye-sauye, ta hanyar janyewa daga yarjeniyoyin kasa da kasa, da ma wasu hukumomin na kasa da kasa.

Labarai Masu Nasaba

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Bugu da kari, binciken na jin ra’ayin jama’a ya nuna cewa, kaso 81.6 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyinsu, na ganin Amurka na kokarin cimma burikan kashin kai ne, ko da kuwa sauran sassan kasa da kasa za su yi hasara, wanda hakan zai yi matukar illata tsarin gaskiya da adalci a fannin jagorancin harkokin duniya, da halastattun moriyar sauran kasashen duniya.

An dora damar bayyana ra’ayoyin ne kan dandalolin kafar CGTN na Turanci, da Faransanci, da Larabci da yaren Sifaniya da na Rasha, inda masu bayyana ra’ayi sama da 7,452 suka kada kuri’unsu cikin sa’o’i 24. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ƙasashe 7 Sun Mara Wa Nijeriya Baya Don Kafa Cibiyar Koyar Da Ilimin Yaɗa Labarai Ta UNESCO – Minista

Next Post

Amurka Ta Manta Da Nauyin Dake Wuyanta Ganin Yadda Ta Janye Daga Yarjejeniyar Sauyin Yanayi Ta Paris

Related

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

4 hours ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

6 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

6 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

10 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

12 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

12 hours ago
Next Post
Amurka Ta Manta Da Nauyin Dake Wuyanta Ganin Yadda Ta Janye Daga Yarjejeniyar Sauyin Yanayi Ta Paris

Amurka Ta Manta Da Nauyin Dake Wuyanta Ganin Yadda Ta Janye Daga Yarjejeniyar Sauyin Yanayi Ta Paris

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.