• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binciken CGTN Ya Nuna Damuwa Daga Sassan Kasa Da Kasa Game Da Yawaitar Ficewar Amurka Daga Yarjeniyoyin Kasa Da Kasa

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
Cgtn

Sabuwar gwamnatin Amurka, ta yi amfani da kwanakinta na farko a kan karaga wajen zartar da jerin umarnin shugaban kasa, inda ta sanar da ficewar Amurka daga yarjejeniyar sauyin yanayi ta Paris, da hukumar lafiya ta duniya WHO, wanda hakan ya haifar da damuwa tsakanin sassan kasa da kasa. 

Wani binciken jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta kasar Sin ta gudanar, ya nuna cewa, manufar nan ta “Sanya Amurka gaban komai”, ba za ta kai kasar zuwa ga sabon “Lokacin cimma Nasarori” ba, kuma hakan zai iya kara haifar da koma baya ga tsarin gudanar da duniya.

  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Inganta Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa A Taron Davos
  • Kwangilar Tashar Wutar Mambila: Obasanjo Zai Bayar Da Shaida A Kotun Paris Yau

Alkaluman sun nuna cewa, kaso 68.5 bisa dari na masu bayyana ra’ayin na ganin janyewar da sabuwar gwamnatin Amurka ta sanar daga yarjejeniyar Paris, da ficewa daga hukumar kiwon lafiya ta duniya WHO, zai gurgunta hadin gwiwar kasa da kasa, a fannin shawo kan sauyin yanayi, da harkokin kula da lafiyar al’umma. Kaza lika, kaso 77.7 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyinsu sun yi matukar damuwa, cewa akwai yiwuwar matakin ya haifar da wani mummunan misali tsakanin kasashen duniya.

Alal hakika, har kullum Amurka na kallon hukumomin kasa da kasa, da cibiyoyi, da tsare-tsaren gudanar da harkokin duniya ta wata mahanga maras dacewa, da kuma idon kare moriyar kashin kai, tana kallon su a matsayin wasu abubuwa na cimma nasara, da tabbatar da manufarta ta danniya a duniya.

Karkashin manufar “Sanya Amurka gaban komai”, sabuwar gwamnatin kasar na kokarin matsawa hukumomin kasa da kasa lamba, ta yadda dole za su yi biyayya ga Amurka kan batutuwa irin su kafa dokoki, da yadda za a gudanar da cibiyoyi da jagorancin sauye-sauye, ta hanyar janyewa daga yarjeniyoyin kasa da kasa, da ma wasu hukumomin na kasa da kasa.

LABARAI MASU NASABA

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Bugu da kari, binciken na jin ra’ayin jama’a ya nuna cewa, kaso 81.6 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyinsu, na ganin Amurka na kokarin cimma burikan kashin kai ne, ko da kuwa sauran sassan kasa da kasa za su yi hasara, wanda hakan zai yi matukar illata tsarin gaskiya da adalci a fannin jagorancin harkokin duniya, da halastattun moriyar sauran kasashen duniya.

An dora damar bayyana ra’ayoyin ne kan dandalolin kafar CGTN na Turanci, da Faransanci, da Larabci da yaren Sifaniya da na Rasha, inda masu bayyana ra’ayi sama da 7,452 suka kada kuri’unsu cikin sa’o’i 24. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26
Daga Birnin Sin

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Next Post
Amurka Ta Manta Da Nauyin Dake Wuyanta Ganin Yadda Ta Janye Daga Yarjejeniyar Sauyin Yanayi Ta Paris

Amurka Ta Manta Da Nauyin Dake Wuyanta Ganin Yadda Ta Janye Daga Yarjejeniyar Sauyin Yanayi Ta Paris

LABARAI MASU NASABA

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.