• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bude Iyakokin Nijeriya Da Nijar: NIS Ta Dage Takunkumin Shige Da Fice

ACG Sunday James Ya Garzaya Yankin Yobe Da Borno Don Tabbatarwa

by yahuzajere
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Bude Iyakokin Nijeriya Da Nijar: NIS Ta Dage Takunkumin Shige Da Fice
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakamakon umarnin da Gwamnatin Tarayya ta bayar na sake buɗe iyakokin Nijeriya da Nijar, Shugabar Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa,  CGI Kemi Nanna Nandap ta Umarci dukkan kwanturololin jihohi da na kula da iyakoki da ke gefen iyakokin Nijeriya da Nijar su tabbatar da aiwatarwa.

Shugabar hukumar ta umarci kwanturololin su ɗage takunkumin shige da ficen mutane da kayayyaki a iyakokin.

Hukumar ta NIS ta tabbatar wa da al’umma cewa a shirye take wajen kula da shige da fice a kan iyakokin Ƙasa bisa ƙa’ida tare da kiyaye mutunci da tsaron iyakokin Nijeriya.

Babban Shugaban Shiyya ta Uku (Zone C), da ta kunshi jihohin Adamawa, Bauchi, Borno, Gombe, Yobe da Filato, Mataimakin Kwanturola Janar (ACG) James Sunday, ya kai ziyarar aiki a jihohin Borno da Yobe da ke Arewa maso Gabas domin lura da yadda ake bude iyakar.

nijar

Labarai Masu Nasaba

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

CGI Kemi Nanna Nandap

A cewar ACG Sunday James, ya garzaya sansanonin gudanar da ayyukan hukumar domin ganin an dauki matakin da ya dace na tabbatar da bude iyakokin ga jama’a ba kuma tare da kawo matsala ga tsaron kasa ba.

A cewar ACG Sunday James, “An sanar da Kwanturola na Yobe da Borno kan wannan umarni, na zo nan a matsayina na shugaban shiyyarsu domin tabbatar da cikakkiyar aiwatar da umarni, tare da tabbatar wa jama’a jajircewarmu wajen tabbatar da tsaron kasa ta hanyar shige da ficen iyakoki a kan ka’ida domin kiyaye mutunci da tsaron ‘Yan Nijeriya.

nijar
Tawagar ACG Sunday James tare da Gwamna Buni da manyan jami’an Gwamnatin Yobe

 

A ranar Laraba ne gwamnatin tarayyar Nijeriya ta umurci hukumomin tsaron kan iyakokin da abin ya shafa da su bude kan iyakar Nijeriya da Nijar a wata sanarwa da mai baiwa shugaban kasa shawara na musamman kan yada labarai, Ajuri Ngelale ya Sanya wa hannu.

Shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin bude iyakokin Nijeriya ta kasa da ta sama da jamhuriyar Nijar tare da dage wasu takunkumin da aka kakabawa kasar nan take.

A cewar sanarwar ta Ajuri Ngelale, umarnin ya yi daidai da shawarar da Kungiyar ECOWAS ta yanke a babban taronta na musamman da ta yi a ranar 24 ga watan Fabrairun 2024 a Abuja.

nijar

Shugabannin ECOWAS sun amince da dage takunkumin karya tattalin arziki da suka kakaba wa Jamhuriyar Nijar, Mali, Burkina Faso, da Guinea.

Daga cikin takunkuman da aka kakaba wa Jamhuriyar Nijar da shugaban kasa ya ba da umarnin dagewa nan take, akwai:

(1) Rufe iyakokin kasa da ta sama tsakanin Nijeriya da Jamhuriyar Nijar, da kuma hana zirga-zirgar jiragen sama a yankunan kasashen ECOWAS daga Nijar zuwa cikinsu ko daga cikinsu zuwa can.

(2) Dakatar da duk wasu hada-hadar kasuwanci da hada-hadar kudi tsakanin Nijeriya da Nijar, da kuma dakatar da duk wasu ayyuka na musamman kamar samar da wuta lantarki ga Jamhuriyar Nijar.

nijar

(3) Rufe kadarorin Jamhuriyar Nijar a Babban Bankin ECOWAS da kadarorin kasar na kamfanonin gwamnati, da ma’aikatu a bankunan kasuwanci.

(4) Dakatar da bai wa Nijar duk wani tallafi na kudi da mu’amala da duk hukumomin kudi, musamman.

(5) Hana tafiye-tafiye ga jami’an gwamnati da iyalansu.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ECOWASIyakokin KasaNijarNijeriyaTakunkumi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ramadan: Gwamna Dauda Ya Biya Ma’aikatan Zamfara Kuɗin Hutu Don Kyautata Walwalarsu

Next Post

Mai Sana’ar POS A Kano Ya Samu Kyautar Naira 500,000 Sakamakon Mayar Da Naira Miliyan 10 Da Aka Tura Bisa Kuskure 

Related

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

8 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

9 hours ago
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban
Manyan Labarai

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

19 hours ago
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi
Manyan Labarai

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

20 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

1 day ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

1 day ago
Next Post
Mai Sana’ar POS A Kano Ya Samu Kyautar Naira 500,000 Sakamakon Mayar Da Naira Miliyan 10 Da Aka Tura Bisa Kuskure 

Mai Sana'ar POS A Kano Ya Samu Kyautar Naira 500,000 Sakamakon Mayar Da Naira Miliyan 10 Da Aka Tura Bisa Kuskure 

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
nijar

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.