ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Bukaci Majalisa Ta Tabbatar Da Nadin Mambobin Majalisar NEDC 12

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Buhari

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya roki Majalisar Dattawa da ta amince da nadin mambobin Majalisar Gudanarwa ta hukumar Bunkasa Shiyyar Arewa Maso Gabas (NEDC) guda 12.

A wata sanarwar da Kakakin shugaban kasan, Malam Garba Shehu ya fitar, Buhari ya roki majalisar ne ta cikin wasikar da ya aike wa shugaban majalisar Dattawa, Ahmed Lawan mai dauke da kwanan wata 3 ga Mayu, 2023.

  • Sudan: Rukuni Na Biyu Na ‘Yan Nijeriya Sun Iso Abuja
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Al’ummar Afirka Ne Ke Da Ikon Tsokaci Kan Hadin-Gwiwar Su Da Kasar Sin

‘‘Bisa dogara da sashin doka bangare na 1, sashi na 2(5)(b) na hukumar bunkasa shiyyar Arewa Maso Gabas (NEDC) ta dokar 2017, ina mai gabatar da jerin sunayen mutanen da na zaba na kuma nada su sha biyu (12) da za su kasance mambobin Majalisar Gudanarwa na hukumar NEDC.

ADVERTISEMENT

‘‘Ya na da kyau Majalisa ta gane cewa wa’adin mambobin Majalisar Gudanarwar hukumar NEDC da ke jagorantar hukumar a halin yanzu zai kare ne a ranar 7 ga watan Mayun 2023,” ya shaida.

Wadanda shugaban ya zaba su ne: Barista Bashir Bukar Baale, a matsayin shugaba, (Arewa Maso Gabas, Yobe), Suwaiba Idris Baba, Darakta mai cikakken iko, sashin kula da harkokin Jin Kai, (Arewa Maso Gabas, Taraba), Musa Umar Yashi, darakta mai cikakken iko a sashin gudanar da mulki da kula da bangaren kudi, (Dan Arewa Maso Gabas ne da ya fito daga jihar Bauchi), Dakta Ismaila Nuhu Maksha, babban darakta Mai cikakken Iko da ke kula da sashin ayyuka, (Arewa Maso Gabas daga jihar Adamawa) da kuma mai-gayya-mai-aiki, Umar Abubakar Hashidu, a matsayin Manajan Gudanarwa kuma babban jami’in gudanarwa (MD/CEO), (Dan Arewa Maso Gabas ne da ya fito daga jihar Gombe).

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Sauran sun hada da: Grema Ali, mamba, (Arewa Maso Gabas, Borno), Onyeka Gospel-Tony, mamba, (Daga Kudu Maso Gabas), Hon. Mrs Hailmary Ogolo Aipoh, mamba, (Dan Kudu Maso Kudu), Air Commodore Babatunde Akanbi (Mai ritaya), mamba (Daga Kudu Maso Yamma ), Mustapha Ahmed Ibrahim, mamba, (Daga Arewa Maso Yamma), Hadiza Maina, mamba, (Arewa ta Tsakiya) da kuma Wakili daga ma’aikatar kudi ya tarayya da kasafi da tsare-tsaren tattalin arziki.

Buhari sai yayi fatan Majalisar za ya yi la’akari da zabinsa tare da amincewa da su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Coas
Manyan Labarai

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal
Labarai

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

November 11, 2025
Next Post
Bikin Canton Fair Ya Samar Da Dimbin Damammakin Kasuwanci

Bikin Canton Fair Ya Samar Da Dimbin Damammakin Kasuwanci

LABARAI MASU NASABA

Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025
CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

November 11, 2025
CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

November 11, 2025
Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

November 11, 2025
CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

November 11, 2025
Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?

Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.