ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sudan: Rukuni Na Biyu Na ‘Yan Nijeriya Sun Iso Abuja

by Sadiq
3 years ago
Sudan

Kashi na biyu na mutanen da aka kwashe sun kunshi ‘yan Nijeriya 130; mata 128 da maza biyu sun isa Abuja ta jirgin saman Tarco.

Da misalin karfe 4 na yamma wadanda aka kwaso suka isa filin jirgin.

  • Qin Gang Ya Halarci Taron Ministocin Wajen Kasashen Kungiyar SCO
  • Bukatar Tafiyar Da Tattalin Arzikin Nijeriya A Dunkule Ta Hanyar Rage Amfani Da Tsabar Kudi

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da babban daraktan hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa (NEMA), Mustapha Ahmed ya ce tuni wasu karin ‘yan Nijeriya 800 ke kan hanyarsu ta zuwa filin jirgin na Masar domin kwaso su zuwa Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Shugaban NEMA, wanda ya tarbi wadanda aka kwaso daga Sudan, ya ce Max Air mai daukar fasinjoji 560 da kuma Azman Air mai daukar fasinjoji 400 tuni suka isa kasar Masar domin jigilarsu.

Ya kuma ce an kulla alaka da jirgin Air Peace da gwamnatin tarayya za ta yi duk mai yiwuwa don kwaso dukkan ‘yan Nijeriya daga Sudan.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Wasu daga cikin wadanda aka kwaso, wadanda suka zanta da LEADERSHIP, sun ce abin ya yi muni matuka, amma sun ji dadin dawowarsu gida.

Daya daga cikinsu wata Hajia Medina ta ce ta yi balaguro zuwa tashar jiragen ruwa na Sudan da kan iyakar Masar cikin mawuyacin hali.

Sai dai ta yaba wa gwamnatin tarayya da ta kawo musu dauki.

Har ila yau, shugaban kafafen yada labarai na NEMA, Ezekiel Manzo ya ce, “Bugu da kari, bisa la’akari da muhimman bukatun al’ummar Nijeriya da ke kan iyakar Masar, NEMA ta ci gaba da samar musu da abinci da ruwa da sauran muhimman kayayyaki a yayin da suke jiran izinin shiga kasar Masar don jigilar su zuwa Najeriya.

“NEMA da Ofishin Jakadancin Nijeriya a Masar ne suka samar da abincin.

“Ta hanyar shigar da wasu kamfanonin jiragen sama, za a kara kaimi wajen kwashe su, haka zalika, Taco aviation da ke Sudan ta himmatu wajen inganta jigilar ‘yan kasarmu zuwa gida daga gabar tashar jiragen ruwan Sudan.

“Babban daraktan NEMA, ya yaba da amincewar da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ba hukumar; domin gudanar da aikin kwaso mutanen.

“Haka zalika, babban daraktan hukumar NEMA ya yaba da irin tallafin da ministar kula da jin kai da agaji da ci gaban al’umma, Hajiya Sadiya Umar Farouq ta bayar.

Ya kuma umarci masu ruwa da tsaki da su ci gaba da hada kai da hukumar NEMA domin tabbatar da cewa an kammala kwaso ‘yan Nijeriya baki daya”.

MASU ALAKA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Next Post
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Al’ummar Afirka Ne Ke Da Ikon Tsokaci Kan Hadin-Gwiwar Su Da Kasar Sin

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Al’ummar Afirka Ne Ke Da Ikon Tsokaci Kan Hadin-Gwiwar Su Da Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.