ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sudan: Rukuni Na Biyu Na ‘Yan Nijeriya Sun Iso Abuja

by Sadiq
3 years ago
Sudan

Kashi na biyu na mutanen da aka kwashe sun kunshi ‘yan Nijeriya 130; mata 128 da maza biyu sun isa Abuja ta jirgin saman Tarco.

Da misalin karfe 4 na yamma wadanda aka kwaso suka isa filin jirgin.

  • Qin Gang Ya Halarci Taron Ministocin Wajen Kasashen Kungiyar SCO
  • Bukatar Tafiyar Da Tattalin Arzikin Nijeriya A Dunkule Ta Hanyar Rage Amfani Da Tsabar Kudi

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da babban daraktan hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa (NEMA), Mustapha Ahmed ya ce tuni wasu karin ‘yan Nijeriya 800 ke kan hanyarsu ta zuwa filin jirgin na Masar domin kwaso su zuwa Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Shugaban NEMA, wanda ya tarbi wadanda aka kwaso daga Sudan, ya ce Max Air mai daukar fasinjoji 560 da kuma Azman Air mai daukar fasinjoji 400 tuni suka isa kasar Masar domin jigilarsu.

Ya kuma ce an kulla alaka da jirgin Air Peace da gwamnatin tarayya za ta yi duk mai yiwuwa don kwaso dukkan ‘yan Nijeriya daga Sudan.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Wasu daga cikin wadanda aka kwaso, wadanda suka zanta da LEADERSHIP, sun ce abin ya yi muni matuka, amma sun ji dadin dawowarsu gida.

Daya daga cikinsu wata Hajia Medina ta ce ta yi balaguro zuwa tashar jiragen ruwa na Sudan da kan iyakar Masar cikin mawuyacin hali.

Sai dai ta yaba wa gwamnatin tarayya da ta kawo musu dauki.

Har ila yau, shugaban kafafen yada labarai na NEMA, Ezekiel Manzo ya ce, “Bugu da kari, bisa la’akari da muhimman bukatun al’ummar Nijeriya da ke kan iyakar Masar, NEMA ta ci gaba da samar musu da abinci da ruwa da sauran muhimman kayayyaki a yayin da suke jiran izinin shiga kasar Masar don jigilar su zuwa Najeriya.

“NEMA da Ofishin Jakadancin Nijeriya a Masar ne suka samar da abincin.

“Ta hanyar shigar da wasu kamfanonin jiragen sama, za a kara kaimi wajen kwashe su, haka zalika, Taco aviation da ke Sudan ta himmatu wajen inganta jigilar ‘yan kasarmu zuwa gida daga gabar tashar jiragen ruwan Sudan.

“Babban daraktan NEMA, ya yaba da amincewar da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ba hukumar; domin gudanar da aikin kwaso mutanen.

“Haka zalika, babban daraktan hukumar NEMA ya yaba da irin tallafin da ministar kula da jin kai da agaji da ci gaban al’umma, Hajiya Sadiya Umar Farouq ta bayar.

Ya kuma umarci masu ruwa da tsaki da su ci gaba da hada kai da hukumar NEMA domin tabbatar da cewa an kammala kwaso ‘yan Nijeriya baki daya”.

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Al’ummar Afirka Ne Ke Da Ikon Tsokaci Kan Hadin-Gwiwar Su Da Kasar Sin

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Al’ummar Afirka Ne Ke Da Ikon Tsokaci Kan Hadin-Gwiwar Su Da Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.