ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sudan: Rukuni Na Biyu Na ‘Yan Nijeriya Sun Iso Abuja

by Sadiq
3 years ago
Sudan

Kashi na biyu na mutanen da aka kwashe sun kunshi ‘yan Nijeriya 130; mata 128 da maza biyu sun isa Abuja ta jirgin saman Tarco.

Da misalin karfe 4 na yamma wadanda aka kwaso suka isa filin jirgin.

  • Qin Gang Ya Halarci Taron Ministocin Wajen Kasashen Kungiyar SCO
  • Bukatar Tafiyar Da Tattalin Arzikin Nijeriya A Dunkule Ta Hanyar Rage Amfani Da Tsabar Kudi

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da babban daraktan hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa (NEMA), Mustapha Ahmed ya ce tuni wasu karin ‘yan Nijeriya 800 ke kan hanyarsu ta zuwa filin jirgin na Masar domin kwaso su zuwa Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Shugaban NEMA, wanda ya tarbi wadanda aka kwaso daga Sudan, ya ce Max Air mai daukar fasinjoji 560 da kuma Azman Air mai daukar fasinjoji 400 tuni suka isa kasar Masar domin jigilarsu.

Ya kuma ce an kulla alaka da jirgin Air Peace da gwamnatin tarayya za ta yi duk mai yiwuwa don kwaso dukkan ‘yan Nijeriya daga Sudan.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Wasu daga cikin wadanda aka kwaso, wadanda suka zanta da LEADERSHIP, sun ce abin ya yi muni matuka, amma sun ji dadin dawowarsu gida.

Daya daga cikinsu wata Hajia Medina ta ce ta yi balaguro zuwa tashar jiragen ruwa na Sudan da kan iyakar Masar cikin mawuyacin hali.

Sai dai ta yaba wa gwamnatin tarayya da ta kawo musu dauki.

Har ila yau, shugaban kafafen yada labarai na NEMA, Ezekiel Manzo ya ce, “Bugu da kari, bisa la’akari da muhimman bukatun al’ummar Nijeriya da ke kan iyakar Masar, NEMA ta ci gaba da samar musu da abinci da ruwa da sauran muhimman kayayyaki a yayin da suke jiran izinin shiga kasar Masar don jigilar su zuwa Najeriya.

“NEMA da Ofishin Jakadancin Nijeriya a Masar ne suka samar da abincin.

“Ta hanyar shigar da wasu kamfanonin jiragen sama, za a kara kaimi wajen kwashe su, haka zalika, Taco aviation da ke Sudan ta himmatu wajen inganta jigilar ‘yan kasarmu zuwa gida daga gabar tashar jiragen ruwan Sudan.

“Babban daraktan NEMA, ya yaba da amincewar da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ba hukumar; domin gudanar da aikin kwaso mutanen.

“Haka zalika, babban daraktan hukumar NEMA ya yaba da irin tallafin da ministar kula da jin kai da agaji da ci gaban al’umma, Hajiya Sadiya Umar Farouq ta bayar.

Ya kuma umarci masu ruwa da tsaki da su ci gaba da hada kai da hukumar NEMA domin tabbatar da cewa an kammala kwaso ‘yan Nijeriya baki daya”.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Al’ummar Afirka Ne Ke Da Ikon Tsokaci Kan Hadin-Gwiwar Su Da Kasar Sin

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Al’ummar Afirka Ne Ke Da Ikon Tsokaci Kan Hadin-Gwiwar Su Da Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.