• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Kafa Hukumar Gudanarwa Ta Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas (NEDC)  

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Buhari Ya Kafa Hukumar Gudanarwa Ta Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas (NEDC)  
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaba Muhammadu Buhari ya kafa hukumar gudanarwa ta Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas (NEDC) mai wakilai goma sha biyu da su ka haɗa da Daraktan Sashen Harkokin Jinƙai a Ma’aikatar Harkokin Jinƙai Agaji da Inganta Rayuwa ta Tarayya, Alhaji Grema Ali.

 

A sanarwar da mai ba ministar harkokin jinƙai shawara kan aikin jarida, Nneka Ikem Anibeze, ta raba a Abuja a ranar Litinin, an bayyana cewa Buhari ya aika da takarda zuwa ga Shugaban Majalisar Dattawa Ahmed Lawan a ranar 3 ga Mayu, 2023, inda ya buƙaci majalisar da ta amince da naɗin sababbin membobin hukumar gudanarwar.

  • Buhari Ya Yi Duk Abin Da Ya Dace Wajen Magance Matsalolin Nijeriya – Shagalinku

Shugaban ƙasar ya ce: ‘‘Kamar yadda Sashe na 1, ƙaramin sashe na 2(5)(b) na Dokar Kafa Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas ta 2017 ya tanadar, ina farin cikin gabatar wa da Majalisar Dattawa mutum 12 da aka zaɓa, kamar yadda aka jero su a nan ƙasa, a matsayin membobin Hukumar Gudanarwa ta Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas.

 

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

‘‘Ina kira ga Majalisar Dattawa da ta lura da cewa wa’adin ‘yan Hukumar Gudanarwar Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas zai ƙare a ranar 7 ga Mayu, 2023.’’

 

Waɗanda aka zaɓa ɗin dai su ne: Lauya Bashir Bukar Baale, Ciyaman (Arewa-maso-gabas, Yobe), Suwaiba Idris Baba, Babbar Darakta, Harkokin Jinƙai (Arewa-maso-gabas, Taraba), Musa Umar Yashi, Babban Daraktan Gudanarwa da Kuɗi (Arewa-maso-gabas, Bauchi), Dakta Isma’ila Nuhu Maksha, Babban Daraktan Ayyuka (Arewa-maso-gabas, Adamawa), da Umar Abubakar Hashidu, Shugaba (Arewa-maso-gabas, Gombe).

 

Sauran su ne Grema Ali, memba (Arewa-maso-gabas, Borno), Onyeka Gospel-Tony, memba (Kudu-maso-gabas), Hon. Madam Hailmary Ogolo Aipoh, memba (Kudu-maso-kudu), Air Commodore Babatunde Akanbi (ritaya), memba (Kudu-maso-yamma), Mustapha Ahmed Ibrahim, memba (Arewa-maso-yamma), Hadiza Maina, memba (Arewa ta Tsakiya), da wakili daga Ma’aikatar Kuɗi, Kasafi da Tsare-tsaren Ƙasa ta Tarayya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fintiri Ya Rantsar Da Mace Ta Farko Babbar Mai Shari’a A Adamawa

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Sako Karin Dalibai 3 Na Kwalejin Jihar Kebbi

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

2 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

3 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

4 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

9 hours ago
Buhari
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

9 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

10 hours ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sako Karin Dalibai 3 Na Kwalejin Jihar Kebbi

'Yan Bindiga Sun Sako Karin Dalibai 3 Na Kwalejin Jihar Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.