• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Kafa Hukumar Gudanarwa Ta Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas (NEDC)  

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Buhari Ya Kafa Hukumar Gudanarwa Ta Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas (NEDC)  
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaba Muhammadu Buhari ya kafa hukumar gudanarwa ta Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas (NEDC) mai wakilai goma sha biyu da su ka haɗa da Daraktan Sashen Harkokin Jinƙai a Ma’aikatar Harkokin Jinƙai Agaji da Inganta Rayuwa ta Tarayya, Alhaji Grema Ali.

 

A sanarwar da mai ba ministar harkokin jinƙai shawara kan aikin jarida, Nneka Ikem Anibeze, ta raba a Abuja a ranar Litinin, an bayyana cewa Buhari ya aika da takarda zuwa ga Shugaban Majalisar Dattawa Ahmed Lawan a ranar 3 ga Mayu, 2023, inda ya buƙaci majalisar da ta amince da naɗin sababbin membobin hukumar gudanarwar.

  • Buhari Ya Yi Duk Abin Da Ya Dace Wajen Magance Matsalolin Nijeriya – Shagalinku

Shugaban ƙasar ya ce: ‘‘Kamar yadda Sashe na 1, ƙaramin sashe na 2(5)(b) na Dokar Kafa Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas ta 2017 ya tanadar, ina farin cikin gabatar wa da Majalisar Dattawa mutum 12 da aka zaɓa, kamar yadda aka jero su a nan ƙasa, a matsayin membobin Hukumar Gudanarwa ta Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas.

 

Labarai Masu Nasaba

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

‘‘Ina kira ga Majalisar Dattawa da ta lura da cewa wa’adin ‘yan Hukumar Gudanarwar Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas zai ƙare a ranar 7 ga Mayu, 2023.’’

 

Waɗanda aka zaɓa ɗin dai su ne: Lauya Bashir Bukar Baale, Ciyaman (Arewa-maso-gabas, Yobe), Suwaiba Idris Baba, Babbar Darakta, Harkokin Jinƙai (Arewa-maso-gabas, Taraba), Musa Umar Yashi, Babban Daraktan Gudanarwa da Kuɗi (Arewa-maso-gabas, Bauchi), Dakta Isma’ila Nuhu Maksha, Babban Daraktan Ayyuka (Arewa-maso-gabas, Adamawa), da Umar Abubakar Hashidu, Shugaba (Arewa-maso-gabas, Gombe).

 

Sauran su ne Grema Ali, memba (Arewa-maso-gabas, Borno), Onyeka Gospel-Tony, memba (Kudu-maso-gabas), Hon. Madam Hailmary Ogolo Aipoh, memba (Kudu-maso-kudu), Air Commodore Babatunde Akanbi (ritaya), memba (Kudu-maso-yamma), Mustapha Ahmed Ibrahim, memba (Arewa-maso-yamma), Hadiza Maina, memba (Arewa ta Tsakiya), da wakili daga Ma’aikatar Kuɗi, Kasafi da Tsare-tsaren Ƙasa ta Tarayya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fintiri Ya Rantsar Da Mace Ta Farko Babbar Mai Shari’a A Adamawa

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Sako Karin Dalibai 3 Na Kwalejin Jihar Kebbi

Related

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar
Labarai

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

9 hours ago
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo
Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

10 hours ago
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

14 hours ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

14 hours ago
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

16 hours ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

17 hours ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sako Karin Dalibai 3 Na Kwalejin Jihar Kebbi

'Yan Bindiga Sun Sako Karin Dalibai 3 Na Kwalejin Jihar Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.