ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Yi Duk Abin Da Ya Dace Wajen Magance Matsalolin Nijeriya – Shagalinku

by Isah Abdullahi
3 years ago
shagalinku

Fitaccen dan kasuwan nan da ke Zariya a Jihar Kaduna, Alhaji Umaru Shagalinku ya kai ziyarar ban girma ga Shugaban kasa, Muhammadu Buhar a fadar gwamna-tin tarayya da ke Abuja.

A lokacin wannan ziyarar, Alhaji Shagalinku ya bayyana cewa Shugaba Buhari ya yi iya bakin kokarinsa wajen kawar da matsalolin da suka addabi Nijeriya.

  • Buhari Ya Bukaci Majalisa Ta Tabbatar Da Nadin Mambobin Majalisar NEDC 12

Ya yaba wa Shugaban Buhari na yadda a shekara takwas da suka gabata ya yi duk abin da ya dace domin kawo karshen matsalolin da suke addabar Nijeriya da ku-ma ‘yan Nijeriya baki daya.

ADVERTISEMENT

Alhaji Shagalinku ya ci gaba da cewa duk wanda ya san halin da Nijeriya ke ciki kafin zaben 2015, ya san Shugaban Buhari ya dauki matakai da dama domin kawo karshen matsalolin tsaro da ke neman durkusar da Nijeriya da kuma ‘yan Nijeriya, amma matakan da Shugaba Buhari ya dauka ya kawo mafita masu yawan gaske ga ‘yan Nijeriya, musamman a jihohin arewa da matsalolin tsaron suka fi yin ka-mari a baya.

A cewar Shagalinku, wadannan matakai da ya fara samun mafita ga matsalolin tsaro yana fatan zai ci gaba da nuna wa zababben shugaban kasa, Alhaji Ahmed Bola Tunubu hanyoyin da ya tsaya a kansu, domin samun mafita na karshe ga matsalolin tsaron Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

A game da bangaren noma kuma, Shagalinku ya ce an sami shekaru masu yawa da gwamnatocin da suka gabata ba su fito da tsare -tsaren da Shugaba Buhari ya fito da su ba, wanda duk wanda ke Nijeriya ya san an sami ci gaba a harkar noma, musamman a bangaren noman shinkafa da suka haifar da da mai ido ga manoman shinkafa a Nijeriya.

Ya shawarci sabon shugaban kasa mai jirar gado da ya dora daga wajen da Shugaban Buhari ya tsaya, domin al’ummar Nijeriya su dogara da shinkafar da ake nomawa a cikin gida.

Da yake mayar da jawabi, Shugaban Buhari ya fara da nuna jin dadinsa da wan-nan ziyara da Alhaji Umaru Shagalinku ya kai ma sa a fadar gwamnatin tarayya a Abuja.

Shugaba Buhari ya kuma yaba wa Alhaji Ummaru Shagalinku na yadda ya kwashe shekaru a harkar kasuwanci a sassan Nijeriya wanda ya samar wa dubban ‘yan Nijeriya sana’o’in dogaro da kai.

Shagalinku
Isah Abdullahi
+ postsBio
  • Isah Abdullahi
    https://hausa.leadership.ng/author/isah-abdullahi/
    Ruftawar Masallacin Fadar Zazzau: Abubuwan Da Suka Kamata A Sani Na Tarihi
  • Isah Abdullahi
    https://hausa.leadership.ng/author/isah-abdullahi/
    Mun Dauki Matakan Fito-na-fito Da Masu Kawo Gurbataccen Taki A Kasuwarmu – Masu Sayar Da Taki
  • Isah Abdullahi
    https://hausa.leadership.ng/author/isah-abdullahi/
    Matsalar Da Mata Ke Ciki Ta Sa Na Rungumi Rubuce-rubuce -Hajiya Hafsat Barau
  • Isah Abdullahi
    https://hausa.leadership.ng/author/isah-abdullahi/
    Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya

MASU ALAKA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano
Siyasa

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

April 25, 2026
Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Next Post
Yaushe Ne Za A Ga Bayan Hare-haren Bindiga A Amurka?

Yaushe Ne Za A Ga Bayan Hare-haren Bindiga A Amurka?

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.