ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Yi Duk Abin Da Ya Dace Wajen Magance Matsalolin Nijeriya – Shagalinku

by Isah Abdullahi
3 years ago
shagalinku

Fitaccen dan kasuwan nan da ke Zariya a Jihar Kaduna, Alhaji Umaru Shagalinku ya kai ziyarar ban girma ga Shugaban kasa, Muhammadu Buhar a fadar gwamna-tin tarayya da ke Abuja.

A lokacin wannan ziyarar, Alhaji Shagalinku ya bayyana cewa Shugaba Buhari ya yi iya bakin kokarinsa wajen kawar da matsalolin da suka addabi Nijeriya.

  • Buhari Ya Bukaci Majalisa Ta Tabbatar Da Nadin Mambobin Majalisar NEDC 12

Ya yaba wa Shugaban Buhari na yadda a shekara takwas da suka gabata ya yi duk abin da ya dace domin kawo karshen matsalolin da suke addabar Nijeriya da ku-ma ‘yan Nijeriya baki daya.

ADVERTISEMENT

Alhaji Shagalinku ya ci gaba da cewa duk wanda ya san halin da Nijeriya ke ciki kafin zaben 2015, ya san Shugaban Buhari ya dauki matakai da dama domin kawo karshen matsalolin tsaro da ke neman durkusar da Nijeriya da kuma ‘yan Nijeriya, amma matakan da Shugaba Buhari ya dauka ya kawo mafita masu yawan gaske ga ‘yan Nijeriya, musamman a jihohin arewa da matsalolin tsaron suka fi yin ka-mari a baya.

A cewar Shagalinku, wadannan matakai da ya fara samun mafita ga matsalolin tsaro yana fatan zai ci gaba da nuna wa zababben shugaban kasa, Alhaji Ahmed Bola Tunubu hanyoyin da ya tsaya a kansu, domin samun mafita na karshe ga matsalolin tsaron Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

A game da bangaren noma kuma, Shagalinku ya ce an sami shekaru masu yawa da gwamnatocin da suka gabata ba su fito da tsare -tsaren da Shugaba Buhari ya fito da su ba, wanda duk wanda ke Nijeriya ya san an sami ci gaba a harkar noma, musamman a bangaren noman shinkafa da suka haifar da da mai ido ga manoman shinkafa a Nijeriya.

Ya shawarci sabon shugaban kasa mai jirar gado da ya dora daga wajen da Shugaban Buhari ya tsaya, domin al’ummar Nijeriya su dogara da shinkafar da ake nomawa a cikin gida.

Da yake mayar da jawabi, Shugaban Buhari ya fara da nuna jin dadinsa da wan-nan ziyara da Alhaji Umaru Shagalinku ya kai ma sa a fadar gwamnatin tarayya a Abuja.

Shugaba Buhari ya kuma yaba wa Alhaji Ummaru Shagalinku na yadda ya kwashe shekaru a harkar kasuwanci a sassan Nijeriya wanda ya samar wa dubban ‘yan Nijeriya sana’o’in dogaro da kai.

Shagalinku
Isah Abdullahi
+ postsBio
  • Isah Abdullahi
    https://hausa.leadership.ng/author/isah-abdullahi/
    Ruftawar Masallacin Fadar Zazzau: Abubuwan Da Suka Kamata A Sani Na Tarihi
  • Isah Abdullahi
    https://hausa.leadership.ng/author/isah-abdullahi/
    Mun Dauki Matakan Fito-na-fito Da Masu Kawo Gurbataccen Taki A Kasuwarmu – Masu Sayar Da Taki
  • Isah Abdullahi
    https://hausa.leadership.ng/author/isah-abdullahi/
    Matsalar Da Mata Ke Ciki Ta Sa Na Rungumi Rubuce-rubuce -Hajiya Hafsat Barau
  • Isah Abdullahi
    https://hausa.leadership.ng/author/isah-abdullahi/
    Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya

MASU ALAKA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano
Siyasa

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

April 25, 2026
Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Next Post
Yaushe Ne Za A Ga Bayan Hare-haren Bindiga A Amurka?

Yaushe Ne Za A Ga Bayan Hare-haren Bindiga A Amurka?

LABARAI MASU NASABA

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.