• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Umarci Shugabannin Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas Da Su Kama Aiki 

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Buhari Ya Umarci Shugabannin Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas Da Su Kama Aiki 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya umarci membobin sabuwar hukumar gudanarwa ta Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas (NEDC) da su kama aikin riƙon ƙwarya ba tare da ɓata lokaci ba don kada a bar wajen babu shugabanni.

 

Shugabannin za su yi aiki ne kafin su samu tabbacin naɗin su daga Majalisar Dattawa kamar yadda doka ta tanada.

  • NSCDC Ta Cafke Mutum 9 Kan Zargin Satar Sinadarin Ruwa A Zamfara

Wata sanarwa ga manema labarai da Babban Sakataren Ma’aikatar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Dakta Nasir Sani-Gwarzo, ya rattaba wa hannu ta ce an yanke wannan shawarar ne don kada a bar wajen babu shugabanni.

 

Labarai Masu Nasaba

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

Haka kuma shugaban ƙasa ya amince da cewa sabon Manajan Darakta kuma Shugaban hukumar, Alhaji Umar Abubakar Hashidu, shi ma ya kama aiki a matsayin riƙo kafin ya samu amincewar Majalisar Dattawa.

 

Dakta Gwarzo ya ce hakan ta faru ne bayan ƙarewar wa’adin tsohon shugaban hukumar da sauran membobin a ranar 7 ga Mayu, 2023.

 

A cewar sa, Buhari ya kuma amince wa Lauya Bukar Baale da ya kama aiki a matsayin ciyaman mai riƙon ƙwarya na hukumar tare da membobi 10 na hukumar gudanarwar.

 

Bugu da ƙari, shugaban ya ba da umarni ga jami’in da ke riƙe da ofishin manajan daraktan hukumar a yanzu da miƙa ragamar ga sabon da aka naɗa ba tare da ɓata lokaci ba.

 

Gwarzo ya ce an ba da wannan umarnin ne domin “a kauce wa samun giɓi a wajen gudanar da ayyukan yau da kullum a wannan hukumar mai matuƙar muhimmanci da tasiri kafin lokacin da Majalisar Dattawa za ta ba su tabbacin naɗin su.”

 

Ita dai Hukumar Gudanarwar ta NEDC ta ƙunshi membobi kamar haka: Suwaiba Idris Baba, Babbar Daraktar Harkokin Agaji (daga Taraba, Arewa-maso-gabas); Musa Umar Yashi, Babban Daraktan Gudanarwa da Harkar Kuɗi (daga Bauchi, Arewa-maso-gabas); Dakta Isma’ila Nuhu Maksha, Babban Daraktan Gudanarwa (daga Adamawa, Arewa-maso-gabas), da Umar Abubakar Hashidu, Manajan Darakta/Shugaba (daga Gombe, Arewa-maso-gabas).

 

Sauran su ne Onyeka Gospel-Tony, Memba, (daga Kudu-maso-gabas); Hon. Madam Hailmary Ogolo Aipoh, Memba (daga Kudu-maso-kudu); Eya Kwamanda Babatunde Akanbi (ritaya), Memba (daga Kudu-maso-yamma); Mustapha Ahmed Ibrahim, Memba (daga Arewa-maso-yamma); Hadiza Maina, Memba (daga Arewa-ta-tsakiya), Alhaji Grema Ali, Memba (daga Arewa-maso-gabas), da kuma wakili daga Ma’aikatar Kuɗi, Kasafi da Tsare-tsaren Ƙasa ta Tarayya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Bikin Ba Da Lambar Yabo Ta Tsarin Gadon Kayayyakin Noma Mai Muhimmanci Na 2023

Next Post

Xi Ya Amsa Wasikar Tsoffin Masanan Dakin Adana Kayayyakin Fasaha Na Sin

Related

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
Da ɗumi-ɗuminsa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

1 hour ago
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

2 hours ago
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

5 hours ago
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi
Da ɗumi-ɗuminsa

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

7 hours ago
Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja
Manyan Labarai

Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

9 hours ago
SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai
Labarai

SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

11 hours ago
Next Post
Xi Ya Amsa Wasikar Tsoffin Masanan Dakin Adana Kayayyakin Fasaha Na Sin

Xi Ya Amsa Wasikar Tsoffin Masanan Dakin Adana Kayayyakin Fasaha Na Sin

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

July 28, 2025
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

July 28, 2025
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

July 28, 2025
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

July 28, 2025
An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

July 28, 2025
Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

July 28, 2025
Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

July 28, 2025
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

July 28, 2025
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

July 28, 2025
Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.