• English
  • Business News
Wednesday, July 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Zai Tafi Portugal Yau Talata Don Halartar Taron Majalisar Dinkin Duniya

by Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
Buhari Ya Sake Shillawa Kasar Ghana Don Halartar Taron ECOWAS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, zai bar Abuja a yau Talata zuwa ziyarar aiki kasar Portugal bisa gayyatar da shugaban kasar, Marcelo Rebelo de Sousa, ya yi masa, kamar yadda fadar shugaban kasar ta bayyana.

Shugaban wanda zai yi wata tattaunawa a hukumance da takwaransa na Portugal, za kuma a ba shi lambar yabo ta kasa da kuma yi masa ado da ‘Great Collar of the Order of Prince Henry’.

  • Buhari Ya Rantsar Da Ariwoola A Matsayin Sabon Alkalin Alkalai Na Kasa
  • Buhari Ya Ce Ba Zai Nemi Wa’adi Na Uku Ba

Wata sanarwa da mai taimaka wa shugaban kasa na musamman kan harkokin yada labarai, Garba Shehu, ya sanya wa hannu a ranar Talata, ta ce ana sa ran shugabannin biyu za su jagoranci wani gagarumin taron kasashen biyu da kulla wasu yarjeniyoyin da suka shafi kan iyakokin kasashen biyu.

Shugaba Buhari zai kuma ziyarci majalisar dokokin kasar Portugal inda zai tattauna da shugabanta Dr Augusto Santo Silva da kuma firaministan kasar Portugal Antonio Costa.

Shehu ya bayyana cewa, a yayin ziyarar, shugaban kasar zai yi jawabi a wani taron ‘yan kasuwan Nijeriya da na kasar Portugal tare da yin ganawa daban-daban da wasu zababbun manyan jami’an gudanarwa na kasar Portugal da masu son zuba jari a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Allah Ya Yi Wa Wakilin Sadarwan Bauchi,  Jafaru Ilelah, Rasuwa

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Katsina, Sun Jikkata Mutane 2, Sun Sace Wasu

Shugaba Buhari zai kuma halarci taron Majalisar Dinkin Duniya a kan teku, wanda aka fara a Lisbon a ranar Litinin, 27 ga watan Yuni, wanda zai gudana har zuwa 1 ga watan Yuli.

Taron, wanda gwamnatocin Kenya da Portugal suka shirya tare da goyon bayan Sashen Tattalin Arziki da Al’uma na Majalisar Ɗinkin Duniya (DESA), na da nufin hanzarta ɗaukar sabbin hanyoyin samar da sabbin hanyoyin kimiyya don fuskantar ƙalubalen da ke fuskantar teku da kuma yanayin ruwa na duniya.

Ana kuma sa ran shugaban na Nijeriya zai tattauna da ‘yan Nijeriya mazauna kasar Portugal kan al’amuran da suka shafe su da kuma abubuwan da ke faruwa a cikin gida.

Shugaban kasar zai samu rakiyar ministan harkokin waje, Geoffrey Onyeama da Ministan yada labarai da al’adu, Lai Mohammed da Ministan Masana’antu, Kasuwanci da Zuba Jari, Adeniyi Adebayo sai Ministan Matasa da Wasanni, Sunday Dare da kuma Ministan Sadarwa, Isa Ali Pantami.

Sauran sun hada da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Maj-Gen Babagana Monguno (rtd) da Darakta Janar na Hukumar Leken Asiri ta Kasa (NIA), Amb. Ahmed Rufa’i Abubakar da shugaban hukumar ‘yan Nijeriya mazauna kasashen waje (NiDCOM) Honorabul Abike Dabiri-Erewa.

Sanarwar ta kara da cewa shugaban zai koma Abuja ranar Asabar 2 ga watan Yuli.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariPortugalShugaba Buharitafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

PDP Ta Ja Kunnen Tsohon Shugaban Kasa, Obasanjo Kan Dan Takararta

Next Post

Ranar Laraba Za A Fara Duban Watan Zul-hijjah A Saudiyya

Related

Allah Ya Yi Wa Wakilin Sadarwan Bauchi,  Jafaru Ilelah, Rasuwa
Labarai

Allah Ya Yi Wa Wakilin Sadarwan Bauchi,  Jafaru Ilelah, Rasuwa

59 minutes ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Katsina, Sun Jikkata Mutane 2, Sun Sace Wasu

2 hours ago
Ɗan Shekaru 15 Ya Kashe Wani Matashi Kan Rikicin Gona A Jigawa
Labarai

Ɗan Shekaru 15 Ya Kashe Wani Matashi Kan Rikicin Gona A Jigawa

3 hours ago
Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

11 hours ago
Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO
Labarai

Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO

12 hours ago
Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

13 hours ago
Next Post
Ranar Laraba Za A Fara Duban Watan Zul-hijjah A Saudiyya

Ranar Laraba Za A Fara Duban Watan Zul-hijjah A Saudiyya

LABARAI MASU NASABA

Allah Ya Yi Wa Wakilin Sadarwan Bauchi,  Jafaru Ilelah, Rasuwa

Allah Ya Yi Wa Wakilin Sadarwan Bauchi,  Jafaru Ilelah, Rasuwa

July 23, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Katsina, Sun Jikkata Mutane 2, Sun Sace Wasu

July 23, 2025
Ɗan Shekaru 15 Ya Kashe Wani Matashi Kan Rikicin Gona A Jigawa

Ɗan Shekaru 15 Ya Kashe Wani Matashi Kan Rikicin Gona A Jigawa

July 23, 2025
Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

July 22, 2025
Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

July 22, 2025
Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO

Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO

July 22, 2025
Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

July 22, 2025
Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

July 22, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Shawarwari Da Tattaunawa

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Shawarwari Da Tattaunawa

July 22, 2025
Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Kwaskwarimar Majalisar Dokoki Kan Naira Biliyan 7

Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Kwaskwarimar Majalisar Dokoki Kan Naira Biliyan 7

July 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.