• English
  • Business News
Monday, October 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Zai Tafi Portugal Yau Talata Don Halartar Taron Majalisar Dinkin Duniya

by Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
Buhari Ya Sake Shillawa Kasar Ghana Don Halartar Taron ECOWAS

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, zai bar Abuja a yau Talata zuwa ziyarar aiki kasar Portugal bisa gayyatar da shugaban kasar, Marcelo Rebelo de Sousa, ya yi masa, kamar yadda fadar shugaban kasar ta bayyana.

Shugaban wanda zai yi wata tattaunawa a hukumance da takwaransa na Portugal, za kuma a ba shi lambar yabo ta kasa da kuma yi masa ado da ‘Great Collar of the Order of Prince Henry’.

  • Buhari Ya Rantsar Da Ariwoola A Matsayin Sabon Alkalin Alkalai Na Kasa
  • Buhari Ya Ce Ba Zai Nemi Wa’adi Na Uku Ba

Wata sanarwa da mai taimaka wa shugaban kasa na musamman kan harkokin yada labarai, Garba Shehu, ya sanya wa hannu a ranar Talata, ta ce ana sa ran shugabannin biyu za su jagoranci wani gagarumin taron kasashen biyu da kulla wasu yarjeniyoyin da suka shafi kan iyakokin kasashen biyu.

Shugaba Buhari zai kuma ziyarci majalisar dokokin kasar Portugal inda zai tattauna da shugabanta Dr Augusto Santo Silva da kuma firaministan kasar Portugal Antonio Costa.

Shehu ya bayyana cewa, a yayin ziyarar, shugaban kasar zai yi jawabi a wani taron ‘yan kasuwan Nijeriya da na kasar Portugal tare da yin ganawa daban-daban da wasu zababbun manyan jami’an gudanarwa na kasar Portugal da masu son zuba jari a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Talaucin Da Ya Ninku Fiye Da Sau Biyu A Gwamnatin Tinubu, An Ƙuduri Aniyar Kawar Da Shi Nan Da Shekaru 5

TRCN Ta Koka Kan Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya 

Shugaba Buhari zai kuma halarci taron Majalisar Dinkin Duniya a kan teku, wanda aka fara a Lisbon a ranar Litinin, 27 ga watan Yuni, wanda zai gudana har zuwa 1 ga watan Yuli.

Taron, wanda gwamnatocin Kenya da Portugal suka shirya tare da goyon bayan Sashen Tattalin Arziki da Al’uma na Majalisar Ɗinkin Duniya (DESA), na da nufin hanzarta ɗaukar sabbin hanyoyin samar da sabbin hanyoyin kimiyya don fuskantar ƙalubalen da ke fuskantar teku da kuma yanayin ruwa na duniya.

Ana kuma sa ran shugaban na Nijeriya zai tattauna da ‘yan Nijeriya mazauna kasar Portugal kan al’amuran da suka shafe su da kuma abubuwan da ke faruwa a cikin gida.

Shugaban kasar zai samu rakiyar ministan harkokin waje, Geoffrey Onyeama da Ministan yada labarai da al’adu, Lai Mohammed da Ministan Masana’antu, Kasuwanci da Zuba Jari, Adeniyi Adebayo sai Ministan Matasa da Wasanni, Sunday Dare da kuma Ministan Sadarwa, Isa Ali Pantami.

Sauran sun hada da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Maj-Gen Babagana Monguno (rtd) da Darakta Janar na Hukumar Leken Asiri ta Kasa (NIA), Amb. Ahmed Rufa’i Abubakar da shugaban hukumar ‘yan Nijeriya mazauna kasashen waje (NiDCOM) Honorabul Abike Dabiri-Erewa.

Sanarwar ta kara da cewa shugaban zai koma Abuja ranar Asabar 2 ga watan Yuli.

Tags: BuhariPortugalShugaba Buharitafiya
ShareTweetSendShare
Muhammad

Muhammad

Related

Tinubu
Manyan Labarai

Talaucin Da Ya Ninku Fiye Da Sau Biyu A Gwamnatin Tinubu, An Ƙuduri Aniyar Kawar Da Shi Nan Da Shekaru 5

2 hours ago
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)
Labarai

TRCN Ta Koka Kan Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya 

4 hours ago
Sojoji Sun Tarwatsa Maɓoyar ‘Yan Bindiga 11, Sun Ƙwato Makamai A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Maɓoyar ‘Yan Bindiga 11, Sun Ƙwato Makamai A Taraba

5 hours ago
Next Post
Ranar Laraba Za A Fara Duban Watan Zul-hijjah A Saudiyya

Ranar Laraba Za A Fara Duban Watan Zul-hijjah A Saudiyya

LABARAI MASU NASABA

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

October 6, 2025
Nazari Ya Gano Falalen Dutse Na Yanki Mai Nisa A Duniyar Wata Ya Fi Tsananin Sanyi Fiye Da Na Yanki Na Kusa

Nazari Ya Gano Falalen Dutse Na Yanki Mai Nisa A Duniyar Wata Ya Fi Tsananin Sanyi Fiye Da Na Yanki Na Kusa

October 6, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025
Tinubu

Talaucin Da Ya Ninku Fiye Da Sau Biyu A Gwamnatin Tinubu, An Ƙuduri Aniyar Kawar Da Shi Nan Da Shekaru 5

October 6, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

TRCN Ta Koka Kan Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya 

October 6, 2025
Rwanda Da Huawei Sun Kaddamar Da Shirin DigiTruck Domin Bunkasa Fasaha A Fadin Kasar

Rwanda Da Huawei Sun Kaddamar Da Shirin DigiTruck Domin Bunkasa Fasaha A Fadin Kasar

October 6, 2025
Sojoji Sun Tarwatsa Maɓoyar ‘Yan Bindiga 11, Sun Ƙwato Makamai A Taraba

Sojoji Sun Tarwatsa Maɓoyar ‘Yan Bindiga 11, Sun Ƙwato Makamai A Taraba

October 6, 2025
Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar

Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar

October 6, 2025
Kwale-kwale

Kifewar Kwale-kwale, Ya Ci Rayukan ‘Yan Uwa 5 A Benuwe 

October 6, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

October 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.