• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Zai Tafi Portugal Yau Talata Don Halartar Taron Majalisar Dinkin Duniya

by Muhammad
3 years ago
Buhari

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, zai bar Abuja a yau Talata zuwa ziyarar aiki kasar Portugal bisa gayyatar da shugaban kasar, Marcelo Rebelo de Sousa, ya yi masa, kamar yadda fadar shugaban kasar ta bayyana.

Shugaban wanda zai yi wata tattaunawa a hukumance da takwaransa na Portugal, za kuma a ba shi lambar yabo ta kasa da kuma yi masa ado da ‘Great Collar of the Order of Prince Henry’.

  • Buhari Ya Rantsar Da Ariwoola A Matsayin Sabon Alkalin Alkalai Na Kasa
  • Buhari Ya Ce Ba Zai Nemi Wa’adi Na Uku Ba

Wata sanarwa da mai taimaka wa shugaban kasa na musamman kan harkokin yada labarai, Garba Shehu, ya sanya wa hannu a ranar Talata, ta ce ana sa ran shugabannin biyu za su jagoranci wani gagarumin taron kasashen biyu da kulla wasu yarjeniyoyin da suka shafi kan iyakokin kasashen biyu.

Shugaba Buhari zai kuma ziyarci majalisar dokokin kasar Portugal inda zai tattauna da shugabanta Dr Augusto Santo Silva da kuma firaministan kasar Portugal Antonio Costa.

Shehu ya bayyana cewa, a yayin ziyarar, shugaban kasar zai yi jawabi a wani taron ‘yan kasuwan Nijeriya da na kasar Portugal tare da yin ganawa daban-daban da wasu zababbun manyan jami’an gudanarwa na kasar Portugal da masu son zuba jari a Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

Shugaba Buhari zai kuma halarci taron Majalisar Dinkin Duniya a kan teku, wanda aka fara a Lisbon a ranar Litinin, 27 ga watan Yuni, wanda zai gudana har zuwa 1 ga watan Yuli.

Taron, wanda gwamnatocin Kenya da Portugal suka shirya tare da goyon bayan Sashen Tattalin Arziki da Al’uma na Majalisar Ɗinkin Duniya (DESA), na da nufin hanzarta ɗaukar sabbin hanyoyin samar da sabbin hanyoyin kimiyya don fuskantar ƙalubalen da ke fuskantar teku da kuma yanayin ruwa na duniya.

Ana kuma sa ran shugaban na Nijeriya zai tattauna da ‘yan Nijeriya mazauna kasar Portugal kan al’amuran da suka shafe su da kuma abubuwan da ke faruwa a cikin gida.

Shugaban kasar zai samu rakiyar ministan harkokin waje, Geoffrey Onyeama da Ministan yada labarai da al’adu, Lai Mohammed da Ministan Masana’antu, Kasuwanci da Zuba Jari, Adeniyi Adebayo sai Ministan Matasa da Wasanni, Sunday Dare da kuma Ministan Sadarwa, Isa Ali Pantami.

Sauran sun hada da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Maj-Gen Babagana Monguno (rtd) da Darakta Janar na Hukumar Leken Asiri ta Kasa (NIA), Amb. Ahmed Rufa’i Abubakar da shugaban hukumar ‘yan Nijeriya mazauna kasashen waje (NiDCOM) Honorabul Abike Dabiri-Erewa.

Sanarwar ta kara da cewa shugaban zai koma Abuja ranar Asabar 2 ga watan Yuli.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
Manyan Labarai

Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya

November 2, 2025
A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
Ra'ayi Riga

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

November 2, 2025
Maganin Nankarwa (3)
Labarai

Maganin Nankarwa (3)

November 2, 2025
Next Post
Ranar Laraba Za A Fara Duban Watan Zul-hijjah A Saudiyya

Ranar Laraba Za A Fara Duban Watan Zul-hijjah A Saudiyya

LABARAI MASU NASABA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya

November 2, 2025
An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu

An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu

November 2, 2025
Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

November 2, 2025
A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

November 2, 2025
Maganin Nankarwa (3)

Maganin Nankarwa (3)

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legas

November 2, 2025
Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

November 2, 2025
Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

November 2, 2025
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano

November 2, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.