• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

BUK Ta Karrama Farfesa Rasheed Bayan Ya Shafe Shekaru 7 A Hukumar NUC Ta Kasa

"Na yi kewar aji sosai kuma yanzu da na dawo, zan ci gaba da gudanar da ayyukana a Jami'ar." — Farfesa Rasheed

by Muhammad
2 years ago
in Labarai
0
BUK Ta Karrama Farfesa Rasheed Bayan Ya Shafe Shekaru 7 A Hukumar NUC Ta Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi bikin dawowar tsohon babban sakataren hukumar kula da jami’o’i ta kasa (NUC), Farfesa Abubakar Adamu Rasheed zuwa jami’ar bayan ya shafe shekaru bakwai a hukumar.

Jami’ar ta shirya gagarumar liyafar murna da dawowarsa gida a ranar Asabar, 8 ga Yuli, 2023.

  • Babban Sakataren Hukumar Kula Da Jami’o’i Ta Kasa (NUC), Farfesa Rasheed, Ya Yi Murabus
  • NUC Ta Daga Darajar Kwalejin Sa’adatu Rimi Zuwa Jami’a A Kano

Babban taro ya kunshi tsofaffin mataimakan shugabanni Jami’ar da manyan jami’an gwamnati da shugabannin tsangayoyi, Daraktoci da shugabannin Sashe-sashe da sauran ‘yan Jami’ar a babban dakin taro na BUK.

Mataimakin shugaban jami’ar Farfesa Sagir Adamu Abbas ya ce hakika jami’ar ta yi matukar farin ciki da maraba da tsohon sakataren hukumar NUC wanda ya bayyana shi a matsayin ma’aikaci da ya gina BUK ta zama ta zamani.

Ya ce Jami’ar Bayero za ta ci gajiya sosai daga dimbin gogewar Farfesa Rasheed musamman a yanzu da Jami’ar ta mayar da hankalinta wajen ganin ta samu nagarta.

Labarai Masu Nasaba

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

A nasa jawabin, Farfesa Abubakar Rasheed, ya ce kyawawan abubuwan da jami’an gudanarwar Jami’ar suka yi masa ya motsa shi, ya kuma kayatar da shi. Ya bayyana cewa har yanzu yana da ragowar shekara 3 da wata daya ya kammala aikinsa a NUC amma ya yanke shawarar janyewa ya koma aji.

Farfesa Rasheed ya ce, “Na yi kewar aji sosai kuma yanzu da na dawo, zan ci gaba da gudanar da ayyukana a Jami’ar.”

Tun da farko a jawabinsa na maraba, Shugaban taron kuma tsohon mataimakin shugaban jami’ar BUK, Farfesa Muhammad Yahuza Bello, ya ce jami’ar ta yi matukar farin ciki da karbar Farfesa Rasheed a hukumance bayan ya shafe shekaru 7 a NUC.

Ya ce Farfesa Rasheed a lokacin da yake rike da mukamin Mataimakin Shugaban Jami’ar ya aiki da nuna gogewa a kusan dukkanin bangarorin Jami’ar kuma ya yi tasiri ga tsarin tafiyar da Jami’o’in Nijeriya a lokacin da yake NUC.

Babban limamin Kano kuma tsohon mataimakin shugaban jami’ar, Farfesa Muhammad Sani Zahraddeen, mataimakin shugaban jami’ar Al-Istiqama, Farfesa Salisu Shehu, tsohon shugaban ASUU na kasa, Dr Nasiru Isa Fagge, tsohon magatakarda, Dr. Sani ne ya gabatar da sakon fatan alheri. Amin Ibrahim, Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Dr. Abdullahi Bichi da Farfesa S.B Ahmad na cikin mahalarta taron liyafar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BUKFarfesa RasheedJami'ar BayerokanoNUC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hajji 2023: Alhazan Kano 9 Sun Ɓarke Da Gudawa A Makkah

Next Post

NiMet Ta Yi Hasashen Samun Zazzafar Rana A Gobe Talata A Jihohin Kano, Katsina Da Sokoto

Related

Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

48 minutes ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

2 hours ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

2 hours ago
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

3 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

5 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

6 hours ago
Next Post
NiMet Ta Yi Hasashen Samun Zazzafar Rana A Gobe Talata A Jihohin Kano, Katsina Da Sokoto

NiMet Ta Yi Hasashen Samun Zazzafar Rana A Gobe Talata A Jihohin Kano, Katsina Da Sokoto

LABARAI MASU NASABA

Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.