ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

BUK Ta Karrama Farfesa Rasheed Bayan Ya Shafe Shekaru 7 A Hukumar NUC Ta Kasa

"Na yi kewar aji sosai kuma yanzu da na dawo, zan ci gaba da gudanar da ayyukana a Jami'ar." — Farfesa Rasheed

by Muhammad
3 years ago
BUK

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi bikin dawowar tsohon babban sakataren hukumar kula da jami’o’i ta kasa (NUC), Farfesa Abubakar Adamu Rasheed zuwa jami’ar bayan ya shafe shekaru bakwai a hukumar.

Jami’ar ta shirya gagarumar liyafar murna da dawowarsa gida a ranar Asabar, 8 ga Yuli, 2023.

  • Babban Sakataren Hukumar Kula Da Jami’o’i Ta Kasa (NUC), Farfesa Rasheed, Ya Yi Murabus
  • NUC Ta Daga Darajar Kwalejin Sa’adatu Rimi Zuwa Jami’a A Kano

Babban taro ya kunshi tsofaffin mataimakan shugabanni Jami’ar da manyan jami’an gwamnati da shugabannin tsangayoyi, Daraktoci da shugabannin Sashe-sashe da sauran ‘yan Jami’ar a babban dakin taro na BUK.

ADVERTISEMENT

Mataimakin shugaban jami’ar Farfesa Sagir Adamu Abbas ya ce hakika jami’ar ta yi matukar farin ciki da maraba da tsohon sakataren hukumar NUC wanda ya bayyana shi a matsayin ma’aikaci da ya gina BUK ta zama ta zamani.

Ya ce Jami’ar Bayero za ta ci gajiya sosai daga dimbin gogewar Farfesa Rasheed musamman a yanzu da Jami’ar ta mayar da hankalinta wajen ganin ta samu nagarta.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

A nasa jawabin, Farfesa Abubakar Rasheed, ya ce kyawawan abubuwan da jami’an gudanarwar Jami’ar suka yi masa ya motsa shi, ya kuma kayatar da shi. Ya bayyana cewa har yanzu yana da ragowar shekara 3 da wata daya ya kammala aikinsa a NUC amma ya yanke shawarar janyewa ya koma aji.

Farfesa Rasheed ya ce, “Na yi kewar aji sosai kuma yanzu da na dawo, zan ci gaba da gudanar da ayyukana a Jami’ar.”

Tun da farko a jawabinsa na maraba, Shugaban taron kuma tsohon mataimakin shugaban jami’ar BUK, Farfesa Muhammad Yahuza Bello, ya ce jami’ar ta yi matukar farin ciki da karbar Farfesa Rasheed a hukumance bayan ya shafe shekaru 7 a NUC.

Ya ce Farfesa Rasheed a lokacin da yake rike da mukamin Mataimakin Shugaban Jami’ar ya aiki da nuna gogewa a kusan dukkanin bangarorin Jami’ar kuma ya yi tasiri ga tsarin tafiyar da Jami’o’in Nijeriya a lokacin da yake NUC.

Babban limamin Kano kuma tsohon mataimakin shugaban jami’ar, Farfesa Muhammad Sani Zahraddeen, mataimakin shugaban jami’ar Al-Istiqama, Farfesa Salisu Shehu, tsohon shugaban ASUU na kasa, Dr Nasiru Isa Fagge, tsohon magatakarda, Dr. Sani ne ya gabatar da sakon fatan alheri. Amin Ibrahim, Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Dr. Abdullahi Bichi da Farfesa S.B Ahmad na cikin mahalarta taron liyafar.

BUK
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
NiMet Ta Yi Hasashen Samun Zazzafar Rana A Gobe Talata A Jihohin Kano, Katsina Da Sokoto

NiMet Ta Yi Hasashen Samun Zazzafar Rana A Gobe Talata A Jihohin Kano, Katsina Da Sokoto

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.