ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

BUK Ta Karrama Farfesa Rasheed Bayan Ya Shafe Shekaru 7 A Hukumar NUC Ta Kasa

"Na yi kewar aji sosai kuma yanzu da na dawo, zan ci gaba da gudanar da ayyukana a Jami'ar." — Farfesa Rasheed

by Muhammad
3 years ago
BUK

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi bikin dawowar tsohon babban sakataren hukumar kula da jami’o’i ta kasa (NUC), Farfesa Abubakar Adamu Rasheed zuwa jami’ar bayan ya shafe shekaru bakwai a hukumar.

Jami’ar ta shirya gagarumar liyafar murna da dawowarsa gida a ranar Asabar, 8 ga Yuli, 2023.

  • Babban Sakataren Hukumar Kula Da Jami’o’i Ta Kasa (NUC), Farfesa Rasheed, Ya Yi Murabus
  • NUC Ta Daga Darajar Kwalejin Sa’adatu Rimi Zuwa Jami’a A Kano

Babban taro ya kunshi tsofaffin mataimakan shugabanni Jami’ar da manyan jami’an gwamnati da shugabannin tsangayoyi, Daraktoci da shugabannin Sashe-sashe da sauran ‘yan Jami’ar a babban dakin taro na BUK.

ADVERTISEMENT

Mataimakin shugaban jami’ar Farfesa Sagir Adamu Abbas ya ce hakika jami’ar ta yi matukar farin ciki da maraba da tsohon sakataren hukumar NUC wanda ya bayyana shi a matsayin ma’aikaci da ya gina BUK ta zama ta zamani.

Ya ce Jami’ar Bayero za ta ci gajiya sosai daga dimbin gogewar Farfesa Rasheed musamman a yanzu da Jami’ar ta mayar da hankalinta wajen ganin ta samu nagarta.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

A nasa jawabin, Farfesa Abubakar Rasheed, ya ce kyawawan abubuwan da jami’an gudanarwar Jami’ar suka yi masa ya motsa shi, ya kuma kayatar da shi. Ya bayyana cewa har yanzu yana da ragowar shekara 3 da wata daya ya kammala aikinsa a NUC amma ya yanke shawarar janyewa ya koma aji.

Farfesa Rasheed ya ce, “Na yi kewar aji sosai kuma yanzu da na dawo, zan ci gaba da gudanar da ayyukana a Jami’ar.”

Tun da farko a jawabinsa na maraba, Shugaban taron kuma tsohon mataimakin shugaban jami’ar BUK, Farfesa Muhammad Yahuza Bello, ya ce jami’ar ta yi matukar farin ciki da karbar Farfesa Rasheed a hukumance bayan ya shafe shekaru 7 a NUC.

Ya ce Farfesa Rasheed a lokacin da yake rike da mukamin Mataimakin Shugaban Jami’ar ya aiki da nuna gogewa a kusan dukkanin bangarorin Jami’ar kuma ya yi tasiri ga tsarin tafiyar da Jami’o’in Nijeriya a lokacin da yake NUC.

Babban limamin Kano kuma tsohon mataimakin shugaban jami’ar, Farfesa Muhammad Sani Zahraddeen, mataimakin shugaban jami’ar Al-Istiqama, Farfesa Salisu Shehu, tsohon shugaban ASUU na kasa, Dr Nasiru Isa Fagge, tsohon magatakarda, Dr. Sani ne ya gabatar da sakon fatan alheri. Amin Ibrahim, Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Dr. Abdullahi Bichi da Farfesa S.B Ahmad na cikin mahalarta taron liyafar.

BUK
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
Next Post
NiMet Ta Yi Hasashen Samun Zazzafar Rana A Gobe Talata A Jihohin Kano, Katsina Da Sokoto

NiMet Ta Yi Hasashen Samun Zazzafar Rana A Gobe Talata A Jihohin Kano, Katsina Da Sokoto

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.