ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

BUK Ta Karrama Farfesa Rasheed Bayan Ya Shafe Shekaru 7 A Hukumar NUC Ta Kasa

"Na yi kewar aji sosai kuma yanzu da na dawo, zan ci gaba da gudanar da ayyukana a Jami'ar." — Farfesa Rasheed

by Muhammad
3 years ago
BUK

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi bikin dawowar tsohon babban sakataren hukumar kula da jami’o’i ta kasa (NUC), Farfesa Abubakar Adamu Rasheed zuwa jami’ar bayan ya shafe shekaru bakwai a hukumar.

Jami’ar ta shirya gagarumar liyafar murna da dawowarsa gida a ranar Asabar, 8 ga Yuli, 2023.

  • Babban Sakataren Hukumar Kula Da Jami’o’i Ta Kasa (NUC), Farfesa Rasheed, Ya Yi Murabus
  • NUC Ta Daga Darajar Kwalejin Sa’adatu Rimi Zuwa Jami’a A Kano

Babban taro ya kunshi tsofaffin mataimakan shugabanni Jami’ar da manyan jami’an gwamnati da shugabannin tsangayoyi, Daraktoci da shugabannin Sashe-sashe da sauran ‘yan Jami’ar a babban dakin taro na BUK.

ADVERTISEMENT

Mataimakin shugaban jami’ar Farfesa Sagir Adamu Abbas ya ce hakika jami’ar ta yi matukar farin ciki da maraba da tsohon sakataren hukumar NUC wanda ya bayyana shi a matsayin ma’aikaci da ya gina BUK ta zama ta zamani.

Ya ce Jami’ar Bayero za ta ci gajiya sosai daga dimbin gogewar Farfesa Rasheed musamman a yanzu da Jami’ar ta mayar da hankalinta wajen ganin ta samu nagarta.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

A nasa jawabin, Farfesa Abubakar Rasheed, ya ce kyawawan abubuwan da jami’an gudanarwar Jami’ar suka yi masa ya motsa shi, ya kuma kayatar da shi. Ya bayyana cewa har yanzu yana da ragowar shekara 3 da wata daya ya kammala aikinsa a NUC amma ya yanke shawarar janyewa ya koma aji.

Farfesa Rasheed ya ce, “Na yi kewar aji sosai kuma yanzu da na dawo, zan ci gaba da gudanar da ayyukana a Jami’ar.”

Tun da farko a jawabinsa na maraba, Shugaban taron kuma tsohon mataimakin shugaban jami’ar BUK, Farfesa Muhammad Yahuza Bello, ya ce jami’ar ta yi matukar farin ciki da karbar Farfesa Rasheed a hukumance bayan ya shafe shekaru 7 a NUC.

Ya ce Farfesa Rasheed a lokacin da yake rike da mukamin Mataimakin Shugaban Jami’ar ya aiki da nuna gogewa a kusan dukkanin bangarorin Jami’ar kuma ya yi tasiri ga tsarin tafiyar da Jami’o’in Nijeriya a lokacin da yake NUC.

Babban limamin Kano kuma tsohon mataimakin shugaban jami’ar, Farfesa Muhammad Sani Zahraddeen, mataimakin shugaban jami’ar Al-Istiqama, Farfesa Salisu Shehu, tsohon shugaban ASUU na kasa, Dr Nasiru Isa Fagge, tsohon magatakarda, Dr. Sani ne ya gabatar da sakon fatan alheri. Amin Ibrahim, Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Dr. Abdullahi Bichi da Farfesa S.B Ahmad na cikin mahalarta taron liyafar.

BUK
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
NiMet Ta Yi Hasashen Samun Zazzafar Rana A Gobe Talata A Jihohin Kano, Katsina Da Sokoto

NiMet Ta Yi Hasashen Samun Zazzafar Rana A Gobe Talata A Jihohin Kano, Katsina Da Sokoto

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.