• English
  • Business News
Saturday, May 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Burikan ‘Yan Nijeriya A 2024

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shekarar da ta gabata ta kasance shekarar da ‘yan Nijeriya ba za su taba mantawa ba. Shekarar 2023 ta zo yayin gabatowar babban zaben kasa ta kuma kammalu ne da harin ta’addancin nan da aka kai a ranar kirsimeti a Jihar Filato.

A daidai lokacin da aka fuskanci matsanancin matsalar tattalin arziki sakamakon shigowar sabuwar gwamnatin shugaban Kasa Bola Tinubu, hakan kuma ya bude kofar tsananta matsalar da al’ummar Nieriya suka ci gaba da fuskanta a cikin shekarar duk kuwa da yekuwar sabunta kwarin gwiwa da gwamnatin take yi wa ‘Yan Nijeriya.
Amma kuma duk da wadannan matsalolin, a wannan shekarar ta 2024 akwai wasu abubuwa da ‘yan Nijeriya ke da burin samu in har ana son su kara samun tabbacin cewa, fatan da suke yi na samun rayuwa mai inganci a Nijeriya a nan gaba ba zai tafi a banza ba.

Na farko shi ne sake fasalin tsari da dokokin zabe da kuma bukatar samar wa bangaren shari’a gurbi a tsarin harkokin siyasar kasar nan. Abubuwan da suka faru a babban zaben 2023 da kuma yadda aka tafiyar da kararrakin zaben a kotuna sun zama abin kunya.

Fafutukar wasu ‘yan Nijeriya da dama da kuma kungiyoyi masu zaman kansu tana bukatar a samar da doka da za ta amince da aikawa da sakamakon zabe daga akwatunan zabe zuwa babbar tashar tattara sakamakon zabe ta INEC don a kauce wa magudin zabe bai kai gaci ba, saboda yadda aka lankwasa dokar ta yadda aka ba INEC damar yin yadda ta gama wajen aikawa da sakamakon zabe.

Yadda INEC ta gudanar da zaben 2023 ya sanya al’umma ke kira tare da bukatar a kara karfafa dokokin zabe ta yadda zai zama dole ta tantance masu kada kuri’a tare da tabbatar da aikawa da sakamakon zabe ta intanet a zabuka masu zuwa a nan gaba.

Labarai Masu Nasaba

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari

Haka kuma a karon farko a Nijeriya, zaben 2023 ya samar da shugaban kasa mai karancin kuri’u. Shugaba Bola Tinubu ya samu nasarar lashe kashi daya bisa uku ne na kuriu’un da aka kada a zaben shugaban kasan da aka yi.
Ya kamata a samar da dokar zaben da za ta samar da wanda ya lashe zabe a zabukan shugaban kasa da na Gwamna ko kuma shugaban karamar hukumar da kuri’un da aka kada akalla da kashi 50 a cikin dari a karon faro ko kuma a zagaye na biyu.

Wasu abubuwan da aka gabatar a yayin sauraron kararrakin zabukan zaben sun kara nuna bukatar a samar da karin canje-canje a dokokin zabe. ‘Yan Nijeriya za su so ganin an wawarware dukkan rikice-rikice da suka taso sakamakon zabukan fidda gwani kafin a gudanar da zabe da kuma ganin an warware dukkan matsalolin da suka taso sakamakon zabukan da aka gudanar kafin a rantsar da wadanda suka samu nasara.
Bayan kasancewa shari’un suna katsalanda ga harkokin gudanar da mulki suna kuma kara wa wanda ake kalubalantar nasararsa karfi a shari’un da ake yi.

Wadanda aka rantsar suna iya amfani da karfin kujerar da suke a kai wajen tabbatar da nasara ga kansu.
‘Yan Nijeriya na kuma bukatar ganin hukumar zabe mai zaman kanta tun daga yadda ake nada manyan jami’anta don kada a fada wa tarkon ‘yan siyasa.
Haka kuma bai kamata a ce, wasu masu shari’a ‘yan kalilan ne suke da hurumin yanke hukuncin wanda ya yi nasara a zabukan da aka gudanar ba.

A wannan tsarin na yanzu an dora wa wasu mashari’a nauyi, wasu kuma daga cikinsu za su iya aikata son rai in har suka samu abin da suke so. Kamar yadda lamarin ke ta kara karuwa, ana iya watsi da kuri’un da al’umma suka kada saboda wasu kalkale-kalkalen shari’a a kotuna.

In har wani mashari’a ya gano wata matsala a zaben da aka yi to ya kamata ne ya umarci a koma wajen al’umma don sake dauko ra’ayoyin al’umma. Dukkan wadanna na bukatar a sake yi wa dokokin zabe kwaskwarima.
Rashin tsaron rayuka da dukiyar al’umma na daga cikin abubuwan da ‘Yan Nijeriya ke fata a kawo karshe a 2024. A wannan kasar da yawa daga cikin masu aikata laifi suna watayawa ba tare da an hukunta su ba.

‘Yan Nijeriya na bukatar ganin jami’an tsaron da za su gano tare da kawo kawo karshen masu aikata laifukka tun daga kananan barayi, manyan ‘yan damfara, ‘yan fashi da makami, masu garkuwa da mutane da kuma ‘yan ta’adda.

Suna fatan ganin jami’an tsaron da za su yi aiki ta hanyar amfani da bayanan sirri da kuma kayan aiki na zamani ba kamar yadda abin yake a halin yanzu ba, in ba haka to maganar Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Sa’ad Abubakar III na cewa, a kullum ‘yan ta’adda na riga jami’an tsaromu shiri zai kasance gaskiya kenan.

Yadda wasu ‘yan ta’adda suka kai hari kauyuka 20 a cikin kwanaki 2 a Jihar Filato ba tare da samun wata turjiya ba daga jami’an tsaromu abu ne da bai kamata a amince da shi ba, ya kamata a tabbatar da an hukunta wani ko wasu da ke da alhakin wannan sakacin in har ana son a dauki gwamnati da muhimmanci.

A kan tattalin arziki, ‘Yan Nijeriya na bukatar ganin an rage musu nauyin matsalar tattalin arzikin da suke fuskanta. Yadda ake samun hauhawar farashin kayayyakin masarufi musamman kayan abinci da ya tashi da kashi 32.8 (a kididdigar da aka yi a ranar 15 ga wata Disamba 2023), yana kara tura al’umma ne zuwa kangin talauci inda fiye da kashi 63 daga cikin al’umma Nijeriya miliyan 133 da aka kiyasta a shekara a 2021 suna cikin kangin talauci.
‘Yan Nijeriya na bukatar gwamnati ta samar da hanyoyin kawo karshen matsalolin tsaro da sassan kasar ke fuskanta.

Haka kuma ‘Yan Nijeriya na bukatar jami’an gwamnati su zama abin misali wajen tafi da harkokinsu, ba zai yiwu su rinka yekuwar al’umma su ci gaba da sadakarwa ba alhali su kuma suna rayuwar bushasha suna kashe kudaden gwamnati ba tare da tausayawa ba.

‘Yan Nijeriya na bukatar gwamanati ta kawo karshen yadda take cin bashi tare da kuma ganin an yi amfani da basukan da aka ciwo ta hanyar da ta kamata.

A halin yanzu Nijeriya na amfani na kashi 95 na kudaden shigarta wajen biyan bashin da ake bin ta. Maimaikon cin bashi, ya kamata Nijeriya ta toshe ayyukan cin hanci da rashawa musamman a ma’aikatu da hukumomin gwamnati musamman ta hanyar aringizon kudaden kwangila da tafiye-tafiye kasashen waje.

Daga karshe ‘yan Nijeriya na bukatar ganin an rungumi akidar nan ta rarraba iko a tsakanin bangarorin gwamnati, yadda aka ba gwamnatin tarayya karfi fiye da kima yana kawo cikas ga ayuyykan yaki da matsalar tsaro da kuma bunkasar yankunan karkara. A matsayinmu na gidan jarida muna yi wa ‘Yan Nijeriya fatan alhairi a shekarar a 2024.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NijeriyaSabuwar Shekara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Allah Ya Daukaka Ambaton Manzon Allah (SAW) A Duniya Da Lahira

Next Post

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Kudiri 120 Cikin Wata Shida – Hon. Tajudeen

Related

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 hours ago
Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari
Labarai

Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari

5 hours ago
Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3
Ilimi

Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

14 hours ago
Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

17 hours ago
Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa
Kananan Labarai

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

18 hours ago
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum
Labarai

‘Yan Ta’adda Na Amfani Da Na’urorin Zamani Daidai Lokacin Da Sojoji Ke Da Karancin Makamai -Zulum

19 hours ago
Next Post
Majalisar Wakilai Ta Amince Da Kudiri 120 Cikin Wata Shida – Hon. Tajudeen

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Kudiri 120 Cikin Wata Shida – Hon. Tajudeen

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (2)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (2)

May 24, 2025
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

May 24, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

May 24, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

May 24, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari

Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari

May 24, 2025
Sin Ta Bukaci Kada Amurka Ta Siyasantar Da Hadin Gwiwar Bangaren Ilimi

Sin Ta Bukaci Kada Amurka Ta Siyasantar Da Hadin Gwiwar Bangaren Ilimi

May 23, 2025
Kamfanoni Masu Jarin Waje Sun Ci Gajiyar Tsarin Kasar Sin Na Samar Da Rangwamen Gwamnati Ta Musayar Sabbin Kayayyaki Da Tsofaffi

Kamfanoni Masu Jarin Waje Sun Ci Gajiyar Tsarin Kasar Sin Na Samar Da Rangwamen Gwamnati Ta Musayar Sabbin Kayayyaki Da Tsofaffi

May 23, 2025
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

May 23, 2025
Sin Da ASEAN Sun Kammala Tattaunawa Game Da Kafa Yankin Ciniki Cikin ‘Yanci

Sin Da ASEAN Sun Kammala Tattaunawa Game Da Kafa Yankin Ciniki Cikin ‘Yanci

May 23, 2025
An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing

May 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.