• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Minista Da Sanatar Abuja

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
10 months ago
in Labarai
0
Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cacar baki ta kaure tsakanin ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike da Sanata Ireti Kingibe mai wakintar mazabar Abuja a zauren majalisar dattawa.

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), ya sha alwashin cewa Sanata Ireti ba za ta koma zauren majalisar dattawa ba a 2027.

  • An Aike Da Ɗan Shekara 67 Gidan Yari Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Mata 2 Fyaɗe Yana Ba Su ₦500 A Bauchi
  • Ya Zama Wajibi Amurka Ta Sauke Nauyin Dake Wuyan Ta Game Da Kasar Afghanistan

Ireti ta tsaya takara a jam’iyyar LP, inda ta doke Philip Aduda na jam’iyyar PDP, wanda ya hau kujerar tun daga 2011 zuwa 2023.

Aduda, wanda a fili yake shirin komawa zauren majalisar dattawa, an gan shi yana zagayawa da Wike a yayin rangadin ayyuka.

Da take magana a wani shirin gidan Talabijin na ARISE, ‘yar majalisar ta ce Wike bai tsanana komai ba ga mutanen Babban Birnin Tarayya Abuja.

Labarai Masu Nasaba

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

Ta ce ayyukan samar da ababen more rayuwa da Wike ya kaddamar ba za su amfanar da talakawa ba, inda ta zargi ministar da rashin nuna damuwa kan warware muhimman batutuwan da suka shafi zamantakewa da tattalin arziki da suka addabi al’ummar Babban Birnin Tarayya Abuja.

Ta ce, “Watakila ministar ya kasance minister ne a ma’aikatar da ba ta da jama’a. Sai dai wani yanayi na musamman na ministan Babban Birnin Tarayya shi ne, baya ga samar da ababen more rayuwa da tituna, dole ne ya yi la’akari da bukatun al’ummar wannan yanki. Wannan shi ne ya bambanta shi da ministan ayyuka, ko wata ma’aikatar.

“Ministan Babban Birnin Tarayya yana nuna kansa kamar wani gwamnan. Kamar yadda mutane suka yi min magana a lokacin da aka kaddamar da wadannan hanyoyin. Sun ce, jama’a na murnan bude tituna a Maitama da kuma Gundumar Abuja ta Tsakiya, yawancin jama’a ba sa zama a wurin. Ba zai iya nuna wani aikin da mutane za su amfana kai tsaye a wuraren da suke zaune.

“Bambancin kenan, kamar dai gwamna ya ce maka ya gina wasu hanyoyi, don haka bai damu da bukatun mutane ba. Su mutanen Abuja suna da bukatoci da ya fi na hanyoyi. Domin al’ummar garin Abuja na fama da rashin ruwa, wutar da sauran abubuwa.”

Da yake mayar da martani, Wike, ya ce ba ya ofis ne don ya faranta mata rai, inda ya kara da cewa ya yi ayyuka masu muhimmanci cikin kankanin lokacin da aka nada minista.

Ministan ya ce sanatan Abuja za ta rasa goyon bayan mazauna Babban Birnin Tarayya Abuja a zaben 2027 mai zuwa.

Wike ya ce, abin takaici ne a ce maimakon ta hada kai da shugabancinsa, amma ta ki yin haka inda ta koma baya tana sukar ayyukansa da na Shugaban kasa, Bola Tinubu.

Ya ce: “Na ji wani shiri a gidan talabijin na Arise TB a safiyar yau. Sai dai kash, ina jin yar majalisar dattawa ce ta fadi haka, kuma abin takaici ta fadi. Tare da girmamawa, abin da ba ka sani ba, ba ka sani ba, abin da ka sani, ka sani.

“Ta ce babu asibitoci kuma akwai. Ke a matsayinki na ‘yar majalisa me ka yi? Nawa kika tallafa mana don inganta fannin ilimi da lafiya?

“Ina kalubalantar sanatan Abuja da cewa, ba za ta dawo wannan kujerar ba a zaben 2027, domin ta rasa magoya baya masu yawa.”

Bayan wannan martini ne, sanadar Abuja ta bayyana cewa Wike bai da kuri’a ko daya a Babbar Birnin Tarayya ballantana ya hana ta sake dawowa wannan kujera.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FCTAGwamnatin TarayyaSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kanana Hukumomin Kano Da Jigawa 23 Na Kan Gaba Wajen Fuskantar Ambaliyar Ruwa – NEMA

Next Post

Biyan Sabon Haraji: Gwamnati Ta Tsame Kananan Kamfanoni Da Manoma

Related

Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

1 hour ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

2 hours ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

2 hours ago
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

3 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

5 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

6 hours ago
Next Post
haraji

Biyan Sabon Haraji: Gwamnati Ta Tsame Kananan Kamfanoni Da Manoma

LABARAI MASU NASABA

Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.