• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Minista Da Sanatar Abuja

bySulaiman and Yusuf Shuaibu
1 year ago
Abuja

Cacar baki ta kaure tsakanin ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike da Sanata Ireti Kingibe mai wakintar mazabar Abuja a zauren majalisar dattawa.

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), ya sha alwashin cewa Sanata Ireti ba za ta koma zauren majalisar dattawa ba a 2027.

  • An Aike Da Ɗan Shekara 67 Gidan Yari Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Mata 2 Fyaɗe Yana Ba Su ₦500 A Bauchi
  • Ya Zama Wajibi Amurka Ta Sauke Nauyin Dake Wuyan Ta Game Da Kasar Afghanistan

Ireti ta tsaya takara a jam’iyyar LP, inda ta doke Philip Aduda na jam’iyyar PDP, wanda ya hau kujerar tun daga 2011 zuwa 2023.

Aduda, wanda a fili yake shirin komawa zauren majalisar dattawa, an gan shi yana zagayawa da Wike a yayin rangadin ayyuka.

Da take magana a wani shirin gidan Talabijin na ARISE, ‘yar majalisar ta ce Wike bai tsanana komai ba ga mutanen Babban Birnin Tarayya Abuja.

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Ta ce ayyukan samar da ababen more rayuwa da Wike ya kaddamar ba za su amfanar da talakawa ba, inda ta zargi ministar da rashin nuna damuwa kan warware muhimman batutuwan da suka shafi zamantakewa da tattalin arziki da suka addabi al’ummar Babban Birnin Tarayya Abuja.

Ta ce, “Watakila ministar ya kasance minister ne a ma’aikatar da ba ta da jama’a. Sai dai wani yanayi na musamman na ministan Babban Birnin Tarayya shi ne, baya ga samar da ababen more rayuwa da tituna, dole ne ya yi la’akari da bukatun al’ummar wannan yanki. Wannan shi ne ya bambanta shi da ministan ayyuka, ko wata ma’aikatar.

“Ministan Babban Birnin Tarayya yana nuna kansa kamar wani gwamnan. Kamar yadda mutane suka yi min magana a lokacin da aka kaddamar da wadannan hanyoyin. Sun ce, jama’a na murnan bude tituna a Maitama da kuma Gundumar Abuja ta Tsakiya, yawancin jama’a ba sa zama a wurin. Ba zai iya nuna wani aikin da mutane za su amfana kai tsaye a wuraren da suke zaune.

“Bambancin kenan, kamar dai gwamna ya ce maka ya gina wasu hanyoyi, don haka bai damu da bukatun mutane ba. Su mutanen Abuja suna da bukatoci da ya fi na hanyoyi. Domin al’ummar garin Abuja na fama da rashin ruwa, wutar da sauran abubuwa.”

Da yake mayar da martani, Wike, ya ce ba ya ofis ne don ya faranta mata rai, inda ya kara da cewa ya yi ayyuka masu muhimmanci cikin kankanin lokacin da aka nada minista.

Ministan ya ce sanatan Abuja za ta rasa goyon bayan mazauna Babban Birnin Tarayya Abuja a zaben 2027 mai zuwa.

Wike ya ce, abin takaici ne a ce maimakon ta hada kai da shugabancinsa, amma ta ki yin haka inda ta koma baya tana sukar ayyukansa da na Shugaban kasa, Bola Tinubu.

Ya ce: “Na ji wani shiri a gidan talabijin na Arise TB a safiyar yau. Sai dai kash, ina jin yar majalisar dattawa ce ta fadi haka, kuma abin takaici ta fadi. Tare da girmamawa, abin da ba ka sani ba, ba ka sani ba, abin da ka sani, ka sani.

“Ta ce babu asibitoci kuma akwai. Ke a matsayinki na ‘yar majalisa me ka yi? Nawa kika tallafa mana don inganta fannin ilimi da lafiya?

“Ina kalubalantar sanatan Abuja da cewa, ba za ta dawo wannan kujerar ba a zaben 2027, domin ta rasa magoya baya masu yawa.”

Bayan wannan martini ne, sanadar Abuja ta bayyana cewa Wike bai da kuri’a ko daya a Babbar Birnin Tarayya ballantana ya hana ta sake dawowa wannan kujera.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
haraji

Biyan Sabon Haraji: Gwamnati Ta Tsame Kananan Kamfanoni Da Manoma

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version