ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Minista Da Sanatar Abuja

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
2 years ago
Abuja

Cacar baki ta kaure tsakanin ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike da Sanata Ireti Kingibe mai wakintar mazabar Abuja a zauren majalisar dattawa.

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), ya sha alwashin cewa Sanata Ireti ba za ta koma zauren majalisar dattawa ba a 2027.

  • An Aike Da Ɗan Shekara 67 Gidan Yari Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Mata 2 Fyaɗe Yana Ba Su ₦500 A Bauchi
  • Ya Zama Wajibi Amurka Ta Sauke Nauyin Dake Wuyan Ta Game Da Kasar Afghanistan

Ireti ta tsaya takara a jam’iyyar LP, inda ta doke Philip Aduda na jam’iyyar PDP, wanda ya hau kujerar tun daga 2011 zuwa 2023.

ADVERTISEMENT

Aduda, wanda a fili yake shirin komawa zauren majalisar dattawa, an gan shi yana zagayawa da Wike a yayin rangadin ayyuka.

Da take magana a wani shirin gidan Talabijin na ARISE, ‘yar majalisar ta ce Wike bai tsanana komai ba ga mutanen Babban Birnin Tarayya Abuja.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Ta ce ayyukan samar da ababen more rayuwa da Wike ya kaddamar ba za su amfanar da talakawa ba, inda ta zargi ministar da rashin nuna damuwa kan warware muhimman batutuwan da suka shafi zamantakewa da tattalin arziki da suka addabi al’ummar Babban Birnin Tarayya Abuja.

Ta ce, “Watakila ministar ya kasance minister ne a ma’aikatar da ba ta da jama’a. Sai dai wani yanayi na musamman na ministan Babban Birnin Tarayya shi ne, baya ga samar da ababen more rayuwa da tituna, dole ne ya yi la’akari da bukatun al’ummar wannan yanki. Wannan shi ne ya bambanta shi da ministan ayyuka, ko wata ma’aikatar.

“Ministan Babban Birnin Tarayya yana nuna kansa kamar wani gwamnan. Kamar yadda mutane suka yi min magana a lokacin da aka kaddamar da wadannan hanyoyin. Sun ce, jama’a na murnan bude tituna a Maitama da kuma Gundumar Abuja ta Tsakiya, yawancin jama’a ba sa zama a wurin. Ba zai iya nuna wani aikin da mutane za su amfana kai tsaye a wuraren da suke zaune.

“Bambancin kenan, kamar dai gwamna ya ce maka ya gina wasu hanyoyi, don haka bai damu da bukatun mutane ba. Su mutanen Abuja suna da bukatoci da ya fi na hanyoyi. Domin al’ummar garin Abuja na fama da rashin ruwa, wutar da sauran abubuwa.”

Da yake mayar da martani, Wike, ya ce ba ya ofis ne don ya faranta mata rai, inda ya kara da cewa ya yi ayyuka masu muhimmanci cikin kankanin lokacin da aka nada minista.

Ministan ya ce sanatan Abuja za ta rasa goyon bayan mazauna Babban Birnin Tarayya Abuja a zaben 2027 mai zuwa.

Wike ya ce, abin takaici ne a ce maimakon ta hada kai da shugabancinsa, amma ta ki yin haka inda ta koma baya tana sukar ayyukansa da na Shugaban kasa, Bola Tinubu.

Ya ce: “Na ji wani shiri a gidan talabijin na Arise TB a safiyar yau. Sai dai kash, ina jin yar majalisar dattawa ce ta fadi haka, kuma abin takaici ta fadi. Tare da girmamawa, abin da ba ka sani ba, ba ka sani ba, abin da ka sani, ka sani.

“Ta ce babu asibitoci kuma akwai. Ke a matsayinki na ‘yar majalisa me ka yi? Nawa kika tallafa mana don inganta fannin ilimi da lafiya?

“Ina kalubalantar sanatan Abuja da cewa, ba za ta dawo wannan kujerar ba a zaben 2027, domin ta rasa magoya baya masu yawa.”

Bayan wannan martini ne, sanadar Abuja ta bayyana cewa Wike bai da kuri’a ko daya a Babbar Birnin Tarayya ballantana ya hana ta sake dawowa wannan kujera.

Abuja
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Abuja
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
haraji

Biyan Sabon Haraji: Gwamnati Ta Tsame Kananan Kamfanoni Da Manoma

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.