• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CAF 2025: Nijeriya Ta Fito A Rukuni Mai Zafi

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Wasanni
0
caf 2025
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tawagar ‘yan wasan Super Eagles ta Nijeriya ta fito a cikin rukuni mai wahala a jada-walin wasannin neman cancantar shiga gasar cin kofin Afirka na shekara ta 2025 da za a buga a kasar Morocco.

Sai dai da alama mai kare kambun gasar Nahiyar Afrika, wato Ibory Coast, za ta iya kaiwa ga gasar ta 2025 da za a yi a Morocco, amma da alama Nijeriya ta fada wani rukuni mai matukar rintsi da wahala.

Raba rukunin da aka yi a Birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu, tawagar Super Eagles ta tsinci kanta cikin rukuni daya da kasashen Benin da Rwanda da kuma kasar Libya.

Yanzu tsohon kocin Nijeriya Gernot Rohr ne ke horar da Benin, kuma ya doke Nijeriya da ci 2-1 a watan jiya a wasannin share fagen shiga gasar kofin duniya ta shekarar 2026.

Hukumar kwallon kafa ta Nijeriya yanzu na neman sabon koci biyo bayan ajiye aikin da Finidi George ya yi wanda ya koma Ribers United. Sai dai har yanzu hukumar kwallon kafa ta kasar ba ta tabbatar da tafiyarsa ba a hukumance.

Labarai Masu Nasaba

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface

Ibory Coast da ta lashe gasar nahiyar karo na uku bayan doke Nijeriya a wasan karshe a watan Fabirairu, za ta fafata da gwarzuwar gasar 2012 Zambia, Sierra Leone da kuma Chadi.

Kocin tawagar Ibory Coast, Emerse Fae ya taimaka wajen raba rukunin da aka yi a Jo-hannesburg kuma ya yi farin ciki da sakamakon inda ya ce sun yi wasa da Zambia a wasan share fagen AFCON na baya, saboda haka sun san tawagarsu sosai da sosai.

Tawagar kasashe 48 din an raba su zuwa rukunai 12 ne zuwa kuma gida hudu, yayin da tawagogi biyu na kowanne rukuni za su samu zuwa Morocco a karshe domin buga gasar.

Masu masaukin baki na da kujerar dindindin a gasar, don haka tawaga daya ake nema a rukunin da suke, wanda ya hada da Gabon, Central African Republic da kuma Leso-tho.

Kamar yadda hukumar kula da gasar cin kofin na Afirka ta tsara, za a yi wasanni shida ne na neman gurbin a watan Satumba da Oktoba da kuma watan Nuwambar wannan shekarar. Za a fara wasan AFCON 2025 a ranar 21 ga watan Disambar shekara mai

zuwa, a kuma yi wasan karshe na gasar a ranar 18 ga watan Janairun shekarar 2026 kamar yadda aka tsara.

Gasar za a buga ta ne lokacin da ake wasannin Firimiyar Ingila na karshen shekara da kuma gasar cin kofin zakarun Turai, sannan wannan ne karon farko da ake buga gasar a watan Nuwamba a tarihi, kuma zai shiga lokacin bikin Kirsimeti da sabuwar shekara.

 

Rukunan samun shiga Afcon 2025

Rukunin A: Tunisia, Madagascar, Comoros, The Gambia.- Rukinin B: Morocco, Ga-bon, Central African Republic, Lesotho.- Rukinin C: Egypt, Cape Berde, Mauritania, Botswana.

Rukinin D: Nigeria, Benin, Libya, Rwanda.- Rukinin E: Algeria, Ekuatorial Guinea, To-go, Liberia.- Rukinin F: Ghana, Angola, Sudan, Nijar.- Rukinin G: Ibory Coast, Zambia, Sierra Leone, Chad.- Rukinin H: DR Congo, Guinea, Tanzania, Ethiopia.- Rukinin I: Mali, Mozambikue, Guinea-Bissau, Eswatini.- Rukinin J: Kamaru, Namibia, Kenya, Zimbabwe.- Rukinin K: South Africa, Uganda, Congo, South Sudan. Rukinin L: Senegal, Burkina Faso, Malawi, Burundi


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CAFMoroccoSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dokar Fansho Ta Majalisar Dokoki: Dokar Son Kai Ko …?Kanun Labarai

Next Post

Jamus Ta Sanar Da Shirin Ficewar Dakarunta Daga Nijar

Related

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City
Wasanni

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

11 hours ago
Boniface
Wasanni

Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface

2 days ago
Ronaldo Ya Samu Kyakkyawar Tarba A Hong Kong
Wasanni

Ronaldo Ya Samu Kyakkyawar Tarba A Hong Kong

3 days ago
Yadda Arsenal Ta Doke Manchester United Da Ci 1-0
Wasanni

Yadda Arsenal Ta Doke Manchester United Da Ci 1-0

5 days ago
Waye Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?
Wasanni

Waye Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?

6 days ago
Me Ya Sa Ciwon ACL Ya Zama Barazana Ga ‘Yan Wasan Kwallo?
Wasanni

Me Ya Sa Ciwon ACL Ya Zama Barazana Ga ‘Yan Wasan Kwallo?

6 days ago
Next Post
jamus

Jamus Ta Sanar Da Shirin Ficewar Dakarunta Daga Nijar

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.