• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CAF 2025: Nijeriya Ta Fito A Rukuni Mai Zafi

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
10 months ago
in Wasanni
0
caf 2025
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tawagar ‘yan wasan Super Eagles ta Nijeriya ta fito a cikin rukuni mai wahala a jada-walin wasannin neman cancantar shiga gasar cin kofin Afirka na shekara ta 2025 da za a buga a kasar Morocco.

Sai dai da alama mai kare kambun gasar Nahiyar Afrika, wato Ibory Coast, za ta iya kaiwa ga gasar ta 2025 da za a yi a Morocco, amma da alama Nijeriya ta fada wani rukuni mai matukar rintsi da wahala.

Raba rukunin da aka yi a Birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu, tawagar Super Eagles ta tsinci kanta cikin rukuni daya da kasashen Benin da Rwanda da kuma kasar Libya.

Yanzu tsohon kocin Nijeriya Gernot Rohr ne ke horar da Benin, kuma ya doke Nijeriya da ci 2-1 a watan jiya a wasannin share fagen shiga gasar kofin duniya ta shekarar 2026.

Hukumar kwallon kafa ta Nijeriya yanzu na neman sabon koci biyo bayan ajiye aikin da Finidi George ya yi wanda ya koma Ribers United. Sai dai har yanzu hukumar kwallon kafa ta kasar ba ta tabbatar da tafiyarsa ba a hukumance.

Labarai Masu Nasaba

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Ibory Coast da ta lashe gasar nahiyar karo na uku bayan doke Nijeriya a wasan karshe a watan Fabirairu, za ta fafata da gwarzuwar gasar 2012 Zambia, Sierra Leone da kuma Chadi.

Kocin tawagar Ibory Coast, Emerse Fae ya taimaka wajen raba rukunin da aka yi a Jo-hannesburg kuma ya yi farin ciki da sakamakon inda ya ce sun yi wasa da Zambia a wasan share fagen AFCON na baya, saboda haka sun san tawagarsu sosai da sosai.

Tawagar kasashe 48 din an raba su zuwa rukunai 12 ne zuwa kuma gida hudu, yayin da tawagogi biyu na kowanne rukuni za su samu zuwa Morocco a karshe domin buga gasar.

Masu masaukin baki na da kujerar dindindin a gasar, don haka tawaga daya ake nema a rukunin da suke, wanda ya hada da Gabon, Central African Republic da kuma Leso-tho.

Kamar yadda hukumar kula da gasar cin kofin na Afirka ta tsara, za a yi wasanni shida ne na neman gurbin a watan Satumba da Oktoba da kuma watan Nuwambar wannan shekarar. Za a fara wasan AFCON 2025 a ranar 21 ga watan Disambar shekara mai

zuwa, a kuma yi wasan karshe na gasar a ranar 18 ga watan Janairun shekarar 2026 kamar yadda aka tsara.

Gasar za a buga ta ne lokacin da ake wasannin Firimiyar Ingila na karshen shekara da kuma gasar cin kofin zakarun Turai, sannan wannan ne karon farko da ake buga gasar a watan Nuwamba a tarihi, kuma zai shiga lokacin bikin Kirsimeti da sabuwar shekara.

 

Rukunan samun shiga Afcon 2025

Rukunin A: Tunisia, Madagascar, Comoros, The Gambia.- Rukinin B: Morocco, Ga-bon, Central African Republic, Lesotho.- Rukinin C: Egypt, Cape Berde, Mauritania, Botswana.

Rukinin D: Nigeria, Benin, Libya, Rwanda.- Rukinin E: Algeria, Ekuatorial Guinea, To-go, Liberia.- Rukinin F: Ghana, Angola, Sudan, Nijar.- Rukinin G: Ibory Coast, Zambia, Sierra Leone, Chad.- Rukinin H: DR Congo, Guinea, Tanzania, Ethiopia.- Rukinin I: Mali, Mozambikue, Guinea-Bissau, Eswatini.- Rukinin J: Kamaru, Namibia, Kenya, Zimbabwe.- Rukinin K: South Africa, Uganda, Congo, South Sudan. Rukinin L: Senegal, Burkina Faso, Malawi, Burundi


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CAFMoroccoSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dokar Fansho Ta Majalisar Dokoki: Dokar Son Kai Ko …?Kanun Labarai

Next Post

Jamus Ta Sanar Da Shirin Ficewar Dakarunta Daga Nijar

Related

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau
Wasanni

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

3 days ago
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 
Wasanni

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

3 days ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

6 days ago
Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro
Wasanni

Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

6 days ago
PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 
Wasanni

PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 

7 days ago
UEFA: Inter Milan Ta Yi Wa Barcelona Kancal
Wasanni

UEFA: An Kai Ruwa Rana Yayin Da Inter Ta Koro Barcelona Gida

1 week ago
Next Post
jamus

Jamus Ta Sanar Da Shirin Ficewar Dakarunta Daga Nijar

LABARAI MASU NASABA

gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.