• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“ChinaTravel” Ya Fahimtar Da Al’ummar Duniya Hakikanin Yanayin Da Ake Ciki A Kasar Sin

by Sulaiman and CGTN Hausa
10 months ago
in Ra'ayi Riga
0
“ChinaTravel” Ya Fahimtar Da Al’ummar Duniya Hakikanin Yanayin Da Ake Ciki A Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakamakon jerin matakan da kasar Sin ta gabatar a baya bayan nan na samar da sauki ga baki da ke zuwa kasar Sin, ciki har da shiga kasar ba tare da biza ba da saukaka wa baki hanyoyin biyan kudi da sauransu, baki da ke zuwa nan kasar don yawon shakatawa na karuwa da gaske, wadanda kuma suka harhada hoton bidiyo na Vlog bisa abubuwan da suka gani da ido, kuma suka watsa ta kafofin sada zumunta. A bidiyoyin da suka dauka, ana iya ganin biranen kasar Sin cikin yanayi mai ni’ima da ma nau’o’in abinci masu dadi, baya ga jirgin kasa mai saurin gaske da motoci marasa matuka da makamantansu, da suka shaida ci gaban al’ummar kasar Sin. 

Duk da bambancin launin fatansu da harsunansu da mahangarsu, amma wadannan baki kusan ra’ayinsu ya zo daya bayan ziyararsu a kasar Sin, wato kasar Sin da suka gani da ido ta sha bamban kwarai da yadda suka zata kafin zuwansu nan kasar. Da yawa daga cikin bakin sun ce, sun sha jin labarai marasa kyau daga bakin ‘yan siyasa da kafofin yada labarai na kasashen yamma, don haka, sun damu sosai kafin su tashi zuwa nan kasar, sai dai bayan isowarsu, sun tarar da cewa, akwai tsaro da saukin rayuwa da ma al’umma masu zafin nama a nan kasar.

  • Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Tare Da Takwaransa Na Kasar Guinea Bissau
  • An Kaddamar Da Dandalin Tattaunawa Na Nishan Kan Wayewar Kan Duniya A Lardin Shandong Na Kasar Sin

A sa’i daya kuma, shirye-shiryen bidiyon da wadannan baki masu yawon shakatawa suka watsa masu lakabin“ChinaTravel” sun samu matukar farin jini ta shafukan kafofin sada zumunta na kasa da kasa, har ma“ChinaTravel” tamkar ya zamanto sirrin yadda wani bidiyo ke iya samun karbuwa. Abin lura shi ne, dimbin ra’ayoyin da masu bibbiyar shafukan suka bayyana sun wuce irin ra’ayoyin da a kan bayyana game da shirye-shiryen yawon shakatawa, inda suka soki kafofin yada labarai na kasashen yamma bisa yadda suka gurbata gaskiya, sun kuma yaba wa masu harhada wadannan shirye-shiryen bidiyo bisa yadda suka taimaka wajen fahimtar da karin al’umma gaskiyar lamarin. Wasu masu bibbiyar shafukan sun kuma bayyana niyyar zuwa kasar Sin don su gani da idonsu. Baya ga haka, wasu baki da suka taba zuwa kasar Sin ko kuma suka shafe wasu lokuta suna rayuwa a kasar sun bayyana ra’ayoyinsu cewa, “Da ba ka ga abubuwa da ido a kasar Sin ba, da ba ka san yadda kafofin yada labarai na kasashen yamma suka kasance abin dariya ba.”

Amma me ya sa wadannan shirye-shiryen bidiyon suka samu matukar karbuwa a shafukan sada zumunta? To dalili shi ne yadda wadannan baki da suka yi yawon shakatawa a kasar Sin suka gyara fahimtar al’umma game da kasar Sin, bisa abubuwan da suka gani da ido a kasar. Wasu baki sun ce, a baya ba su samu cikakkiyyar fahimtar kasar Sin ba, kusan ba su iya koyon kome ba game da kasar Sin a makaranta, kuma bayanan da suka samu daga kafofin yada labarai da ‘yan siyasa shi ne “kasar Sin na da koma baya, kasa ce mai hadari, kuma kasa ce mai sharri.” Amma da suka zo nan kasar, sun tarar da cewa, sam sam kasar ba haka ba ce.

Dalilin da ya sa “ChinaTravel” ke matukar samun karbuwa shi ne sabo da irin al’adun kasar mai dadadden tarihi da ma yadda al’ummar kasar ke karbar baki da hannu biyu-biyu, haka kuma sabo da irin niyyar kasar Sin ta dada bude kofarta ga duniya. Muna fatan karin aminanmu ‘yan Afirka za su samu damar zuwa kasar Sin, sabo da kamar yadda Bahaushe kan ce, gani ya kori ji, da zuwanku nan za ku iya fahimtar hakikanin yanayin da ake ciki a kasar.

Labarai Masu Nasaba

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Kasar Sin na muku lale marhabi.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kasar ainPhilippinesYawon shakatawa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rahotanni Biyu Sun Tabbatar Da Cewa Philippines Kasa Ce Dake Bata Muhallin Tekun Kudancin Kasar Sin

Next Post

Gwamnantin Zamfara Za Ta Gina Babbar Tashar Mota Ta Zamani A Gusau

Related

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci
Ra'ayi Riga

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

3 days ago
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

5 days ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

6 days ago
Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba
Ra'ayi Riga

Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba

7 days ago
Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
Ra'ayi Riga

Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya

2 weeks ago
Bai Dace A Mika Wuya Ga Wanda Ya Nuna Fin Karfi Da Matakan Haraji Ba
Ra'ayi Riga

Bai Dace A Mika Wuya Ga Wanda Ya Nuna Fin Karfi Da Matakan Haraji Ba

2 weeks ago
Next Post
Gwamnantin Zamfara Za Ta Gina Babbar Tashar Mota Ta Zamani A Gusau

Gwamnantin Zamfara Za Ta Gina Babbar Tashar Mota Ta Zamani A Gusau

LABARAI MASU NASABA

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.