ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, September 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
CIIE

Shi dai bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin ta kasa da kasa (CIIE) wani dandali ne inda kamfuna, kungiyoyi da kasashe ke taruwa su baje kolin irin kayan da suke da shi, ko kuma irin hidimomin da suke samarwa.

Kasar Sin, wadda ita ce kasa ta biyu mafi karfin tattalin arziki a duniya, ta gudanar da bikin baje koli ta kasa da kasa (CIIE) a kan kayan da ake shigar da su kasar Sin tun daga ranar 5 ga wannan wata na Nuwamba har zuwa 10 ga watan a birnin Shanghai dake yankin gabashin kasar. Kimanin kasashe 17 ne daga Afirka suka samu halartar wannan gagarumin bikin tare da kafa rumfunansu domin baje kolinsu.

Nijeriya ba wai ta kasance daya daga cikin wadannan kasashe ba kadai, har ma an karrama ta da matsayin daya daga cikin manyan baki a wajen wannan taron baje koli.

ADVERTISEMENT

Babu shakka ba abin mamaki ne ba kan irin wannan karramawa da ta samu, musamman idan muka yi la’akari da irin kyakkyawar alaka dake tsakanin kasashen biyu. Misali akwai alakar cinikayya kan amfanin gona kamar su Yazawa, Ridi da Cocoa, wadanda ake shigar da su kasar Sin. Irin wadannan amfanin gona suna daga cikin kolin da Najeriya ta baje a wajen wannan gagarumin taro. Baya ga amfanin gona, Nijeriya ta baje kolin al’adunta ta hanyar baje kolin tufafi da nau’ikan abincinta.

Wannan bikin baje koli ya kara jaddada aniyar kasar Sin ta bude kofarta ga kowa da kowa, musamman kasashen Afirka. Bugu da kari, Sin ta kuduri aniyar cire duk wani haraji kan kayayyakin da ake shigar da su Sin daga kasashen Afirka da suka kulla huldar diplomasiyya da ita, sabanin irin matakan rashin mutunci na rubanya harajin cinikayya da America ke yi kan kayayyakin da ake shigar da su kasar.

LABARAI MASU NASABA

Ra’ayin Kasar Sin Kan Fasahar AI Yana Samar Da Damammaki Ga Afirka

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Babban abin lura a nan shi ne irin alfanun da Nijeriya za ta samu tare da sauran kasashen Afrika daga wannan bikin baje koli.

Na farko dai Nijeriya da sauran kasashen Afirka za su kara kaimi wajen noman irin waɗannan amfanin gona domin fitar da su zuwa Sin, hakan kuwa zai kara samar da aikin yi ga dubban ‘yan Nijeriya, abin da zai habaka kudaden shiga ga kasa.

Alfanu na biyu kuma shi ne fadada damar ingantawa da kara daga darajar irin wadannan amfanin gona da Nijeriya ke samarwa.

Sannan kuma akwai batun bunkasa dangantakar cinikayya tsakanin Sin da Nijeriya da ma sauran kasashen Afirka.

Sabo da haka wannan irin lamari na bude kofar cudanya tsakanin Sin da sauran kasashen duniya, musamman kasashe masu tasowa na Afirka, abin jinjinawa ga kasar Sin, kuma abin koyi ne ga sauran kasashen yammacin duniya. (Lawal Mamuda)

CIIE
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Na Hanyar Siliki Karo Na 13 A Xi’an
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yadda Hadin Gwiwar BRICS Ke Ingiza Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Kammala Taro Na 13 Na Dandalin Tattauna Tsaro Na Xiangshan A Beijing
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Mataimakin Firaministan Sin Ya Halarci Bikin Bude Baje Kolin Sin Da ASEAN Na 23
CIIE
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Pate Ya Jinjina Wa Sauye-sauye Da Inganta Harkokin Lafiya A Katsina
  • Sulaiman
    An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Na Hanyar Siliki Karo Na 13 A Xi’an
  • Sulaiman
    Ko Kano Pillars Za Su Iya Taka Wa Doma United Burki A Yau?
  • Sulaiman
    An Bude Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Asiya Karo Na 20 A Nagoya Na Japan

MASU ALAKA

Ra’ayin Kasar Sin Kan Fasahar AI Yana Samar Da Damammaki Ga Afirka
Ra'ayi Riga

Ra’ayin Kasar Sin Kan Fasahar AI Yana Samar Da Damammaki Ga Afirka

September 14, 2026
Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Next Post
Xi Ya Gana Da Sarkin Sifaniya A Birnin Beijing

Xi Ya Gana Da Sarkin Sifaniya A Birnin Beijing

LABARAI MASU NASABA

Pate Ya Jinjina Wa Sauye-sauye Da Inganta Harkokin Lafiya A Katsina

Pate Ya Jinjina Wa Sauye-sauye Da Inganta Harkokin Lafiya A Katsina

September 20, 2026
An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Na Hanyar Siliki Karo Na 13 A Xi’an

An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Na Hanyar Siliki Karo Na 13 A Xi’an

September 20, 2026
Ko Kano Pillars Za Su Iya Taka Wa Doma United Burki A Yau?

Ko Kano Pillars Za Su Iya Taka Wa Doma United Burki A Yau?

September 20, 2026
An Bude Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Asiya Karo Na 20 A Nagoya Na Japan

An Bude Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Asiya Karo Na 20 A Nagoya Na Japan

September 20, 2026
Trump Ya Hana CNN Da Wasu Kafofin Yaɗa Labarai Shiga Fadar White House

Trump Ya Hana CNN Da Wasu Kafofin Yaɗa Labarai Shiga Fadar White House

September 19, 2026
Adadin Tafiye-Tafiyen Da Jiragen Kasa Masu Jigilar Fasinjoji Suka Yi A Sin Ya Kai Matsayin Koli A Watanni 8 Na Bana

Adadin Tafiye-Tafiyen Da Jiragen Kasa Masu Jigilar Fasinjoji Suka Yi A Sin Ya Kai Matsayin Koli A Watanni 8 Na Bana

September 19, 2026
Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Bauchi Ta Yi Allah-wadai Da Kama Masu Kaɗa Ƙuri’a

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Bauchi Ta Yi Allah-wadai Da Kama Masu Kaɗa Ƙuri’a

September 19, 2026
Kungiyar ’Yan Kasuwar Kaduna Ta Rantsar Da Sabon Shugaban Riƙo

Kungiyar ’Yan Kasuwar Kaduna Ta Rantsar Da Sabon Shugaban Riƙo

September 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD

Sin Na Fatan Inganta Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD

September 19, 2026
Rikicin Fili: Harsashi Ya Yi Ajalin Ɗalibin Jami’a A Neja

Rikicin Fili: Harsashi Ya Yi Ajalin Ɗalibin Jami’a A Neja

September 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.