• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Kasar Sin Zaburarwa Ce Ba Barazana Ba

by Sulaiman
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ci Gaban Kasar Sin Zaburarwa Ce Ba Barazana Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatar harkokin wajen kasar ta bayyana a jiya Litinin cewa, yaudarar cin zarafi da ’yan siyasar Amurka ke yi na kara tsanani. Wannan ya biyo bayan zargin da ’yan siyasar Amurka ke ci gaba da yadawa cewa, na’urorin fasahar sadarwa da batiran motoci masu amfani da wutar lantarki da kasar Sin ke kerawa, na barazana ga tsaron kasa.

Da alama dai, Amurka ta dage wajen ganin ta shafawa kasar Sin bakin fenti ta kowane hali. A baya, Amurka ta kasance mai juya kasashen duniya yadda ta ga dama saboda fa’idojin da take da su da fasahohin da ta mallaka, amma saurin ci gaban da kasa mai tasowa kamar Sin ta samu, bisa dukkan alamu, na tsone mata ido.

  • Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Tsarin Ddoka Da Matakan Yaki Da Taaddanci
  • Klaus Schwab: Davos Yana Fatan Duniya Ta Sake Gina Aminci

Ba tun a yau ’yan siyasar kasar suke yayata batun “barazana ga tsaron kasa” ba, amma har zuwa yau din, babu wata shaida ko hujja da ta tabbatar da zargin nasu. Maimakon haka, kiyayyar da Amurka ke yi da ci gaban kasar Sin ne ke kara fitowa bisa la’akari da yadda take dagewa wajen ganin ta dakile kasar Sin ta kowace hanya.

Hausawa kan ce “Wutsiyar rakumi ta yi nesa da kasa”. Kasar Sin ta yi nisa a fagen raya kanta cikin aminci ta hanyoyi daban-daban, kuma bisa dogaro da albarkatun da ta mallaka. Ci gaban kasar Sin da fasahohinta sun kasance abun zaburarwa da ma taimako ga kasashen duniya, har ita kanta Amurka.

A yanzu, ci gaban kasar Sin ya zama madogara da abun taimako ga kasashe masu tasowa domin ita ba ta kyashin ganin wani ya ci gaba, wanda daya ne daga cikin abun da Amurka ba ta son gani.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Sin kan raba fasahohinta ga kasashe masu tasowa bisa girmama juna kuma ba tare da sharadi ba, wanda shi ne abun da kasashe masu karamin karfi ke bukata na tada komadar tattalin arzikinsu. Shin wannan shi ne “barazana ga tsaron kasa”?

Idan har za a dauki raya kai da taimako a matsayin “barazana ga tsaron kasa” ban san me za a kira “tsoma baki cikin harkokin gida” da “yada jita-jita” da “yunkurin rarraba kawuna” ba, wadanda Amurka ke kan gaba wajen aiwatarwa.

Kamar yadda na fada a baya, ci gaban kasar Sin zaburarwa ce ga kasashen duniya, don haka kamata ya yi Amurka ta dauki darasi ta kuma yi kokarin lalubo hanyoyin raya kanta da kanta ba tare da mulkin mallaka ko ci da gumin wasu ba. Ko ba komai, kasar Sin ta nunawa duniya cewa, akwai hanyoyin samun ci gaba cikin aminci da lumana.(Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alakar Sin da AfirkaCi gaban kasar sinTattalin arzikin kasar Sin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ana Fargabar Kashe Mutane Da Dama Tare Da Kona Gidaje A Sabon Rikicin Filato

Next Post

Sin Ta Ba Da Rahoton Fadada Shigo Da Kayayyakin Gona Da Na Abinci A Shekarar 2023

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

2 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

3 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

5 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

6 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

13 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

15 hours ago
Next Post
Sin Ta Ba Da Rahoton Fadada Shigo Da Kayayyakin Gona Da Na Abinci A Shekarar 2023

Sin Ta Ba Da Rahoton Fadada Shigo Da Kayayyakin Gona Da Na Abinci A Shekarar 2023

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.