• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Kasar Sin Zaburarwa Ce Ba Barazana Ba

by Sulaiman
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ci Gaban Kasar Sin Zaburarwa Ce Ba Barazana Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatar harkokin wajen kasar ta bayyana a jiya Litinin cewa, yaudarar cin zarafi da ’yan siyasar Amurka ke yi na kara tsanani. Wannan ya biyo bayan zargin da ’yan siyasar Amurka ke ci gaba da yadawa cewa, na’urorin fasahar sadarwa da batiran motoci masu amfani da wutar lantarki da kasar Sin ke kerawa, na barazana ga tsaron kasa.

Da alama dai, Amurka ta dage wajen ganin ta shafawa kasar Sin bakin fenti ta kowane hali. A baya, Amurka ta kasance mai juya kasashen duniya yadda ta ga dama saboda fa’idojin da take da su da fasahohin da ta mallaka, amma saurin ci gaban da kasa mai tasowa kamar Sin ta samu, bisa dukkan alamu, na tsone mata ido.

  • Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Tsarin Ddoka Da Matakan Yaki Da Taaddanci
  • Klaus Schwab: Davos Yana Fatan Duniya Ta Sake Gina Aminci

Ba tun a yau ’yan siyasar kasar suke yayata batun “barazana ga tsaron kasa” ba, amma har zuwa yau din, babu wata shaida ko hujja da ta tabbatar da zargin nasu. Maimakon haka, kiyayyar da Amurka ke yi da ci gaban kasar Sin ne ke kara fitowa bisa la’akari da yadda take dagewa wajen ganin ta dakile kasar Sin ta kowace hanya.

Hausawa kan ce “Wutsiyar rakumi ta yi nesa da kasa”. Kasar Sin ta yi nisa a fagen raya kanta cikin aminci ta hanyoyi daban-daban, kuma bisa dogaro da albarkatun da ta mallaka. Ci gaban kasar Sin da fasahohinta sun kasance abun zaburarwa da ma taimako ga kasashen duniya, har ita kanta Amurka.

A yanzu, ci gaban kasar Sin ya zama madogara da abun taimako ga kasashe masu tasowa domin ita ba ta kyashin ganin wani ya ci gaba, wanda daya ne daga cikin abun da Amurka ba ta son gani.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Sin kan raba fasahohinta ga kasashe masu tasowa bisa girmama juna kuma ba tare da sharadi ba, wanda shi ne abun da kasashe masu karamin karfi ke bukata na tada komadar tattalin arzikinsu. Shin wannan shi ne “barazana ga tsaron kasa”?

Idan har za a dauki raya kai da taimako a matsayin “barazana ga tsaron kasa” ban san me za a kira “tsoma baki cikin harkokin gida” da “yada jita-jita” da “yunkurin rarraba kawuna” ba, wadanda Amurka ke kan gaba wajen aiwatarwa.

Kamar yadda na fada a baya, ci gaban kasar Sin zaburarwa ce ga kasashen duniya, don haka kamata ya yi Amurka ta dauki darasi ta kuma yi kokarin lalubo hanyoyin raya kanta da kanta ba tare da mulkin mallaka ko ci da gumin wasu ba. Ko ba komai, kasar Sin ta nunawa duniya cewa, akwai hanyoyin samun ci gaba cikin aminci da lumana.(Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alakar Sin da AfirkaCi gaban kasar sinTattalin arzikin kasar Sin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ana Fargabar Kashe Mutane Da Dama Tare Da Kona Gidaje A Sabon Rikicin Filato

Next Post

Sin Ta Ba Da Rahoton Fadada Shigo Da Kayayyakin Gona Da Na Abinci A Shekarar 2023

Related

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

27 minutes ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

31 minutes ago
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II
Daga Birnin Sin

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

2 hours ago
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

4 hours ago
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”
Daga Birnin Sin

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

4 hours ago
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi
Daga Birnin Sin

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

6 hours ago
Next Post
Sin Ta Ba Da Rahoton Fadada Shigo Da Kayayyakin Gona Da Na Abinci A Shekarar 2023

Sin Ta Ba Da Rahoton Fadada Shigo Da Kayayyakin Gona Da Na Abinci A Shekarar 2023

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.