• English
  • Business News
Thursday, September 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin A Watannin Farkon Bana Zai Kara Karfafa Gwiwa A Duniya

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin A Watannin Farkon Bana Zai Kara Karfafa Gwiwa A Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

Najeriya: Ajandar Jagorantar Duniya Ta Ba Da Gudummawa Ga Tsarin Kasashen Duniya

A baya-bayan nan, sassan gwamnatin kasar Sin sun fitar da alkaluma game da ma’aunan tattalin arziki 3 da suka hada da na yawan kayayyakin da masana’antu ke sayarwa, da na bangaren kasuwanci da bai shafi samar da kayayyaki ba, da kuma na samarwa da fitar da kayayyakin, wadanda suka karu da kaso 1.7 da 1.6 da 1.8 idan aka kwatanta da makamancin lokacin a bara.

Na tuna yadda a lokacin da gwamnatin kasar Sin ta gabatar da rahoton aiki da bayyana burinta na samun karuwar tattalin arziki da kaso 5 a bana, na ji da kunnena wasu kafafen yada labaran yammacin duniya na cewa, kasar Sin ba ta bayyana yadda za a yi ta samu wannan ci gaba ba. Wato kamar su na ganin wannan burin ba mai yuwuwa ba ne. Amma wadannan alkaluma da aka gabatar sun nuna cewa, kasar Sin ta san abun da take yi kuma ta na da yakinin cimma burikan da ta sanya a gaba. A matsayin wadda ta shafe shekaru a kasar Sin, na san kasar ba ta sanya burin da ba za ta iya cimmawa ba, ko in ce, ban ma taba ganin ta sanya wani buri da ta gagara cimmawa ba.

  • Sin Da Faransa Sun Amince Da Gina Alaka Bisa Daidaito Da Hangen Nesa 

Ci gaban da Sin ta samu cikin wadannan watanni, bai tsaya kadai ga wadannan ma’aunai 3 ba, an kuma samu bunkasar wasu manyan fannoni kamar na samar da hidimomi da rayuwar al’umma da sayyaya da sauransu. Abun da irin wadancan kafofin watsa labarai da na bayyana a baya ba su gane ba shi ne, tattalin arzikin kasar Sin na bisa tubali mai kwari dake da juriya. Haka kuma, kasar ba ta dogara da kasashen waje wajen raya tattalin arzikinta ba, domin kasar Sin ta mayar da hankali ne wajen amfani da albarkatun da ta mallaka a cikin gida da kyawawan dabarun da suka dace da ita, da kuma fasahohi da karfinta na kirkire-kirkire. Misali, a cikin bangarorin da suka samu ci gaba, akwai rayuwar al’umma da karuwar sayayya a cikin gida. Kyautatuwar rayuwar al’umma na nufin samun kwanciyar hankali da biyan bukatu da kuma samuwar wadata. Samuwar wadata kuma shi ne ke kara ingiza sayyaya da kashe kudi a cikin gida, wanda ke bayar da gudunmuwa ga tattalin arziki. A ganina, wadannan ci gaba da aka samu cikin kankanin lokaci, somin tabi ne na irin ci gaban da za a kai ga cimmawa zuwa karshen shekara. Haka kuma, ba kasar Sin kadai za ta amfana ba, domin wannan sakamako da aka samu a lokaci kalilan, ba karfafa gwiwar duniya kadai zai yi ba, har ma da samar da makoma mai haske ga tattalin arzikin duniya kamar yadda ya saba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci GabaDuniyaKwarin GwiwaTattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilin Da Yasa Bana Wasa Da Abinci Yayin Daukar Fim – Hadizan Saima

Next Post

An Gano Dajin Da Ya Fi Shekara Miliyan Hudu A Duniya

Related

Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

53 minutes ago
Najeriya: Ajandar Jagorantar Duniya Ta Ba Da Gudummawa Ga Tsarin Kasashen Duniya
Daga Birnin Sin

Najeriya: Ajandar Jagorantar Duniya Ta Ba Da Gudummawa Ga Tsarin Kasashen Duniya

5 hours ago
Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Daga Birnin Sin

Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

21 hours ago
Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

22 hours ago
Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin

23 hours ago
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron CIFTIS Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron CIFTIS Na Shekarar 2025

24 hours ago
Next Post
An Gano Dajin Da Ya Fi Shekara Miliyan Hudu A Duniya

An Gano Dajin Da Ya Fi Shekara Miliyan Hudu A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

September 11, 2025
Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Boko Haram Na Yin TikTok, Suna Sarrafa Jirage Marasa Matuƙi Don Sa Ido Kan Sansanonin Soji – Bulama 

Ƙwararren Masanin Tsaro, Bulama Ya Ƙaryata Iƙirarin El-Rufai Kan Biyan ’Yan Bindiga Kuɗaɗen Fansa

September 11, 2025
Wata Mahanga Ta Daban Na Kallon Ayyukan Ta’addanci

Wata Mahanga Ta Daban Na Kallon Ayyukan Ta’addanci

September 11, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

September 11, 2025
Najeriya: Ajandar Jagorantar Duniya Ta Ba Da Gudummawa Ga Tsarin Kasashen Duniya

Najeriya: Ajandar Jagorantar Duniya Ta Ba Da Gudummawa Ga Tsarin Kasashen Duniya

September 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

Cutar Diphtheria Ta Kashe Yara 10 A Jihar Neja

September 11, 2025
DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

September 11, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Fashi 3 A Kano, Sun Ƙwato Motar Sata

September 11, 2025
Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.