• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin A Watannin Farkon Bana Zai Kara Karfafa Gwiwa A Duniya

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin A Watannin Farkon Bana Zai Kara Karfafa Gwiwa A Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

A baya-bayan nan, sassan gwamnatin kasar Sin sun fitar da alkaluma game da ma’aunan tattalin arziki 3 da suka hada da na yawan kayayyakin da masana’antu ke sayarwa, da na bangaren kasuwanci da bai shafi samar da kayayyaki ba, da kuma na samarwa da fitar da kayayyakin, wadanda suka karu da kaso 1.7 da 1.6 da 1.8 idan aka kwatanta da makamancin lokacin a bara.

Na tuna yadda a lokacin da gwamnatin kasar Sin ta gabatar da rahoton aiki da bayyana burinta na samun karuwar tattalin arziki da kaso 5 a bana, na ji da kunnena wasu kafafen yada labaran yammacin duniya na cewa, kasar Sin ba ta bayyana yadda za a yi ta samu wannan ci gaba ba. Wato kamar su na ganin wannan burin ba mai yuwuwa ba ne. Amma wadannan alkaluma da aka gabatar sun nuna cewa, kasar Sin ta san abun da take yi kuma ta na da yakinin cimma burikan da ta sanya a gaba. A matsayin wadda ta shafe shekaru a kasar Sin, na san kasar ba ta sanya burin da ba za ta iya cimmawa ba, ko in ce, ban ma taba ganin ta sanya wani buri da ta gagara cimmawa ba.

  • Sin Da Faransa Sun Amince Da Gina Alaka Bisa Daidaito Da Hangen Nesa 

Ci gaban da Sin ta samu cikin wadannan watanni, bai tsaya kadai ga wadannan ma’aunai 3 ba, an kuma samu bunkasar wasu manyan fannoni kamar na samar da hidimomi da rayuwar al’umma da sayyaya da sauransu. Abun da irin wadancan kafofin watsa labarai da na bayyana a baya ba su gane ba shi ne, tattalin arzikin kasar Sin na bisa tubali mai kwari dake da juriya. Haka kuma, kasar ba ta dogara da kasashen waje wajen raya tattalin arzikinta ba, domin kasar Sin ta mayar da hankali ne wajen amfani da albarkatun da ta mallaka a cikin gida da kyawawan dabarun da suka dace da ita, da kuma fasahohi da karfinta na kirkire-kirkire. Misali, a cikin bangarorin da suka samu ci gaba, akwai rayuwar al’umma da karuwar sayayya a cikin gida. Kyautatuwar rayuwar al’umma na nufin samun kwanciyar hankali da biyan bukatu da kuma samuwar wadata. Samuwar wadata kuma shi ne ke kara ingiza sayyaya da kashe kudi a cikin gida, wanda ke bayar da gudunmuwa ga tattalin arziki. A ganina, wadannan ci gaba da aka samu cikin kankanin lokaci, somin tabi ne na irin ci gaban da za a kai ga cimmawa zuwa karshen shekara. Haka kuma, ba kasar Sin kadai za ta amfana ba, domin wannan sakamako da aka samu a lokaci kalilan, ba karfafa gwiwar duniya kadai zai yi ba, har ma da samar da makoma mai haske ga tattalin arzikin duniya kamar yadda ya saba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci GabaDuniyaKwarin GwiwaTattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilin Da Yasa Bana Wasa Da Abinci Yayin Daukar Fim – Hadizan Saima

Next Post

An Gano Dajin Da Ya Fi Shekara Miliyan Hudu A Duniya

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

17 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

17 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

19 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

20 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

1 day ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

1 day ago
Next Post
An Gano Dajin Da Ya Fi Shekara Miliyan Hudu A Duniya

An Gano Dajin Da Ya Fi Shekara Miliyan Hudu A Duniya

LABARAI MASU NASABA

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.